Saturday, 18 February 2017

Kadara Tariga Fata Daga Comrade Abubakar Ismail kankara

Ita hidima ta rayiwar Dan Adam, Allah ne ke tsarata duk dacewa shi Dan Adam Mai guri ne da Kuma fatan yasama abunda Zuciyarsa take bukuta a kodayaushe.

Aduk lokacin da wani guri nasa yacika saikuma ya kara hangen wata damar wacce zatakasance gurinsa. Daka wanan lokacin saikuma tunanin maharsada da masoya yazama wani bangaren tunanin Dan Adam.

Dazaran tunanin makiya da maharsada yarinjaye tunanin masoya Sai Kuma wasu matakan hada Kariya takowace hanya domin Samun nasara akowace hidima ta rayiwar.

Itakuma rayiwar takasance rigar aro sabilida duk matsayin Dan Adam baya iya sayanta Saidai ya ingantata da abunda Ubangiji Allah yabashi ikon samar Mata.

Anma duk da haka al'uma sukan Mata cewa Ubangiji Allah shikebadawa Kuma shike karba Aduk lokacin dayaso, Sai su ringa alakanta dukan wani alamari gawani Dan Adam na nasarar ko rashin nasarar.

Monday, 13 February 2017

LABARI: Donald Trump Zai Yi Magana Da Buhari Ta Waya


Fadar shugaban kasar Amurka-White House tace shugaban Amurka Donald Trump zai yi Magana da shugabannin Najeriya da Afirka ta Kudu ta wayar tarho yau Litinin.

Tattaunawar da shugaba Trump zai yi da takwaransa na Najeriya Muhammadu Buhari yana daukar hankali saboda da ba a ji daga Buhari ko kuma ganinsa a bainar jama’a ba tunda ya tafi jinya London ranar goma sha tara ga watan Janairu.

Sabon shugaban kasar Amurka bai yi Magana a kan Afrika ko kuma batutuwa da suka shafi Afrika ba tunda ya hau karagar mulki watan da ya shige. Babu wani bayani daga fadar White House kan abinda shugabannin zasu tattauna a kai. http://bit.ly/2lBLPnW

Domin Karin Bayani: www.voahausa.com


 

Friday, 10 February 2017

Kokarin Gwamna Masari Ya Inganta Rayuwar Matasa A Katsina —Hon. Tanimu Sada

HONARABLE TANIMU SADA SA’AD, Shi ne Mai baiwa Gwamnan Jihar Katsina, Aminu Bello Masari Shawara Kan Ayyuka na Musamman, kuma Shugaban Kungiyar fafitukar ci gaban Matasan Jahar Katsina wato “House-To-House Youth Awareness Forum” (HHYAF). A tattaunawarsa da manema labarai ciki har da Wakilin Leadership Hausa, SAGIR ABUBAKAR a Katsina, Hon. Tanimu ya yi dogan bayani kan makasudin kafa wannan kungiya da kuma batutuwan siyasa da harkokin gwamnati, gami da irin ci gaban da gwamnatinsu karkashin jagorancin Gwamna Aminu Bello Masari ta samu a kasa da shekaru biyu. Ga yadda hirar ta kasance:

Za mu so ka gabatar mana da kanka?

Bissimillah Rahamanin Rahim. Sunana Tanimu Sada Sa’ad, haifaffen cikin garin Katsina ne. Yanzu haka ni ne mai baiwa Gwamna Aminu Bello Masari shawara kan ayyuka na musamman da kuma ayyukan da suka shafi Majalisar Dokoki ta Jihar Katsina.
Duk da kai ne mai baiwa gwamna shawara kan ayyuka na musamman, sai ga shi ka kafa wannan kungiya ta House-To-House Youth Awareness, ko wadanne dalilai ne suka jawo hankalinka ka kafa ta?

Gwamna Masari Ya Kai Ziyarr Duba Ayyukan Tsanyoyi Tare Da Hon.Tanimu Sada


Mai Girma Gwamnan Katsina Rt. Hon Aminu bello Masari ya kai ziyarar gani ido domin duba ayyukan tsanyoyi da a ke aikin su a yau Asabar da misalin karfe 2:26AM.

Mai ba Gwamnan Shawara akan ayyuka na musamman Hon. Tanimu Sada ya baiyana hakan a shafin shi na Facebook akan yanar gizo-gizo.

Tuesday, 7 February 2017

Kotu Ta Daga Shari'ar Tsakanin Shema Da EFCC Zuwa 21 Febuwari, Amma EFCC TA Sake Kamashi A Yanzu Haka


Alkalin dake shari'ar tsakanin tsohon gwamna Barrister Ibrahim Shehu Shema da Hukumar EFFC Maikaita Bako ya dage karar zuwa 21/2/2017.

Labari Da Tumin Sa | APC A Malumfashi Ta Dakatar Dan Majalissar Tarayya Hon. Babangida Mahuta-Karanta Dalili

Hon. Babangida Mahuta
Shugabannin jam'iyyar APC na kananan hukumomin Malumfashi da Kafur sun tsaida wakilinsu a majalissar tarayya.

Shugabannin jam'iyyar Alh. Samaila Garba Sabuwar Kasa da Alh. Yahuza Musa sunce wakilinsu Hon. Babangida Ibrahim Mahuta ya furta wasu kalamai a wajen taron da akayi na jam'iyyar na batanci ga gwamna, rashin ladabi da biyayya ga shugabanni inda wadanda sun saba ma manufofin jam'iyyar.

Sunday, 5 February 2017

ASIBITOCIN KATSINA | KASHE MUTUM A LABORATORIES Daga Teburin Edita | Sani Hamza Funtua.

Jahar Katsina na daya daga cikin manyan Jahohi a yankin Arewacin kasar Nigeria ta fuskoki daban-daban. Babbar fuskar da zamu dauka a wannan karon, itace fuskar Lafiya, fuskar da wannan jaha tayi fice a ciki.

Daga kowacce karamar hukuma, akalla akan samu Manya da kananan Asibitoci Goma (sama-ko-kasa da hakan). Sannan an wadatar da wadannan asibitoci da kwararrun Likitoci da kuma Ma’aikatan Jinya da ke aiki ba dare ba rana.

Duk da kokarin da gwamnatin Jiha keyi na ganin ta gyara wannan fanni na Lafiya a fadin jahar, zamu iya cewa “Ana daure gaba ana Kwance baya” ne, domin kuwa, babban bangaren da yafi kusan kowanne bangare a cikin Asibiti na fuskantar kalubalen da ke haddasa mutuwar Majinyata ba tare da sanin dalili ba a fadin Jihar. Dakin gwaji da nazarin Jini da cututtuka “Laboratory”, shine daki mafi kusa da kusa da muhimmanci a dakunan asibiti. Duk wata cuta wacce za’a yi nazarinta, akan yi nazarin ne a wannan daki. Mafi akasarin cutukan da ake nazarinsu a wannan dakin sun shafi cutuka dake yawo ko rayuwa a cikin Jini. Wannan Jarida ta CLIQQ MAGAZINE ta samu bakuncin Buhari Shehu Faskari, wanda ya bayyana takaicin sa kan yadda ake yiwa wannan Sashe rikon sakainar kashi.

“Ba’a dade ba a cikin jahar Katsina, aka samu wani asibiti da ya sanyawa Wani Yaro Mara lafiya Jinin da ke ‘Karya Garkuwar dan Adam (HIV).” Cewar Buhari Shehu Faskari. Ya ci gaba da cewa: “Da yawa daga cikin ma’aikatan dake aiki a wannan sashi a asibitocin Jahar Katsina, basu cancanta suyi aiki a sashen ba. Zaka ga mutum yayi karatu a Makarantar Kimiyya da Fasaha (Polytechnics), inda aka basu horo don suyi aiki a Dakunan nazari na Cemistry ko Biology a makarantun Sakandire, sune ake turawa dakunan nazari da awon jinni na asibitoci.

Wednesday, 1 February 2017

"Kungiyar House To House Na Kowa Dan Kowa Don Cigaban Jihar Katsina"-Sako Daga Tanimu Sada


Sanarwa!Sanarwa!!Sanarwa!!!

Amadadin kungiyar House to House muna sanar da dukan nin matasan jihar katsina cewa ga dama tasamu wadda kowa zaya bada gudunuwarsa domin kawo cigaban matasan jiharmu batareda Bambancin akida ba koko jinsi madamar manufar ka ki bata sabawa dokar Allah ba ko dokar kasar nan ko jihar mu ba to muna bukatar gudumuwar ku domin mu kowa yanada amfani kuma muna son shi saboda haka madamar kishirya to muna jiranka.

Karanta Cikakken Jawabin Alh Umaru TATA Daya Yi A Oficin PDP Na Katsina


JAWABIN MAIGIRMA ALH. UMAR ABDU TSAURI (TATA) A WURIN TARON KARBA TARE DA KADDAMAR DASHI DA MAGOYA BAYAN SHI CIKIN JAM’IYAR PDP. RANAR TALATA, 31/01/2017, A BABBAN DAKIN TARO NA SAKATARIYAR JAM’IYAR PDP DAKE GARIN KATSINA, A JIHAR KATSINA.