Daga kowacce karamar hukuma, akalla akan samu
Manya da kananan Asibitoci Goma (sama-ko-kasa da hakan). Sannan an wadatar da
wadannan asibitoci da kwararrun Likitoci da kuma Ma’aikatan Jinya da ke aiki ba
dare ba rana.
Duk da kokarin da gwamnatin Jiha keyi na
ganin ta gyara wannan fanni na Lafiya a fadin jahar, zamu iya cewa “Ana daure
gaba ana Kwance baya” ne, domin kuwa, babban bangaren da yafi kusan kowanne
bangare a cikin Asibiti na fuskantar kalubalen da ke haddasa mutuwar Majinyata
ba tare da sanin dalili ba a fadin Jihar. Dakin gwaji da nazarin Jini da
cututtuka “Laboratory”, shine daki mafi kusa da kusa da muhimmanci a dakunan
asibiti. Duk wata cuta wacce za’a yi nazarinta, akan yi nazarin ne a wannan
daki. Mafi akasarin cutukan da ake nazarinsu a wannan dakin sun shafi cutuka
dake yawo ko rayuwa a cikin Jini. Wannan Jarida ta CLIQQ MAGAZINE ta samu
bakuncin Buhari Shehu Faskari, wanda ya bayyana takaicin sa kan yadda ake yiwa
wannan Sashe rikon sakainar kashi.
“Ba’a dade ba a cikin jahar Katsina, aka samu
wani asibiti da ya sanyawa Wani Yaro Mara lafiya Jinin da ke ‘Karya Garkuwar
dan Adam (HIV).” Cewar Buhari Shehu Faskari. Ya ci gaba da cewa: “Da yawa daga
cikin ma’aikatan dake aiki a wannan sashi a asibitocin Jahar Katsina, basu
cancanta suyi aiki a sashen ba. Zaka ga mutum yayi karatu a Makarantar Kimiyya
da Fasaha (Polytechnics), inda aka basu horo don suyi aiki a Dakunan nazari na
Cemistry ko Biology a makarantun Sakandire, sune ake turawa dakunan nazari da
awon jinni na asibitoci.
“Ire-iren wadannan mutane bai kamata a same
su suna aiki a Dakunan gwaji da nazari na Asibitoci ba, domin su [Technologst]
ne kawai. Idan aka sanya su aiki a asibitoci, karshe sai su kasance suna samar
da sakamakobn karya, ko kuma su sauya jinin mai lafiya da jinin mai wata cuta.
“Da yawan su na samun aiki a Asibitoci ne ta
hanyar yin Aikin sa kai (Voluntary), ko kuma idan aka tashi tura aiki, mai
makon a tura su Dakin gwaji da nazari na Makarantu, sai su samu hanya a tura su
Asibitoci.”
Comr. Buhari Shehu Faskari sai kuma ya yi
kira ga Hukumar Lafiya tare da bayyana hanyoyin da za’a bi don magance afkuwar
wannan matsalar, inda yake cewa:
“Hukumar Lafiya ta Jihar Katsina ya kamata ta
fara tantance dakunan Awo da Gwaji a asibitocin dake a fadin Jihar. Wannan
tantancewar ne zai bada damar sanin dakunan awo da keda karancin kayan aiki, ko
kuma wadanda SAM ! ba’a ma san da wanzuwarsu ba.
Comr. Buhari Faskari ya ci gaba da cewa:
“Wadanda ya kamata suyi aiki a dakin Awo da Nazari na asibitoci sune masu
matakin karatu na: Medical Laboratory Assistant Medical Laboratory Technician
Medical Laboratory Scientist “Duk wani karatun Lafiya ana yinsa ne a makarantu
irin su: School of Health Technology Universities in Faculty of Medicine.
“Tantancewar da Hukumar Lafiya zatayi a
bangaren dakin Awo a asibitocin Jahar zai magance sanyawa Marasa Lafiyan da
basu-ji-ba-basu-gani-ba jini mai dauke da cutuka. Fitar da sakamako mara
inganci, da kuma sanadiyyar rasa rayuka.” Daga karshe Comr. Buhari Shehu
Faskari ya bukaci Hukumar Lafiya ta Jahar Katsina dama Gwamnatinm Jiha akan
hukunta duk wanda aka kama ba tare da izinin yin aiki a dakunan awo na awo na
asibitoci ba. “Sannan ya kamata Kwamitin Lafiya na Majalisai Jaha su samar da
doka wacce zata kare wannan kuduri na samar da ingantaccen tsari a dakunan awo
na asibitoci don kare asarar rayuka a fadin jihar”
CLIQQ Magazine na daukar ra’ayoyin makaranta
musamman Yan Asalin Jahar Katsina dama makwaftan jaha. Burin wannan Magazine ta
isar da sakon Al’umma ga shuwagabanninta tare da wayarwa Al’umma kai akan
ayyuka da manufofin Gwamnatin Jaha daman a Tarayya baki daya. Karshen Rahoton
kenan…
Sani Hamza Funtua |
EDITA. 07032183026
No comments:
Post a Comment