Wednesday, 1 February 2017

"Kungiyar House To House Na Kowa Dan Kowa Don Cigaban Jihar Katsina"-Sako Daga Tanimu Sada


Sanarwa!Sanarwa!!Sanarwa!!!

Amadadin kungiyar House to House muna sanar da dukan nin matasan jihar katsina cewa ga dama tasamu wadda kowa zaya bada gudunuwarsa domin kawo cigaban matasan jiharmu batareda Bambancin akida ba koko jinsi madamar manufar ka ki bata sabawa dokar Allah ba ko dokar kasar nan ko jihar mu ba to muna bukatar gudumuwar ku domin mu kowa yanada amfani kuma muna son shi saboda haka madamar kishirya to muna jiranka.

Sannan inaso nasanar daku cewa zamu fara ayyukannmu kwanan nan saboda haka kowa yazo kada yamakara domin a fara dakai.

Kungiyar Gida da Gida wadda aka assasata don wayar ma Jama’ar jihar Katsina, Nigeria dama Duniya gaba daya [House to House Awareness Campaign] akan mahimman aiyuka da za su taimaki al’ummar jihar Katsina.

Kuma ita wannan kungiya ba tada wani alaka da jam’iyar ka ko asalin ka,  kungiyace wadda bazata nuna banbanci tsakanin masoyan gwamnatin APC, PDP,APGA, PDM da dai sauransu.

Kungiya ce wadda gurinta shine ta yaya za a bun kasa jihar Katsina gaba daya a ban garori daban daban irinsu

·        Bada gudunmuwa don bunkasa ilimin jihar katsina.

·        Bada Gudunmuwa ta fannin kiwon lafiya ga asibitocin mu.

·        Talafa ma matasa maza da mata domin dogaro dakai wajen kuyan sana’a daban daban

·        Tattaunawa da mutanen jihar Katsina don sauraren ra’ayoyinsu akan yadda gwamnati zata ‘yanganta rayuwarsu.

 

Sako daga naku har kullum Hon Tanimu sada saad.

 

No comments:

Post a Comment