Sunday, 15 May 2016

Yaushe Jami'an Gwamnati Zasu Fara Zuwa Asibitoci Na Gwamnati-Mallam Mansur

Wai yaushe jami'ai da mukarraban gwamnati zasu fara zuwa asibitoci mallakar gwamnati idan basu lafiya su da zuriyar su?

Lafiya da ilimin al'umma abubuwane masu muhimmanci a rayuwa dan babu abinda ke yiwuwa saida lafiya koda lafiyar kuma saida ilimi, ya kamata kamar yadda adalin shugaba gwamnan wannan jihar yasha alwashin maida ya'yayenshi makarantun al'umma mallakin gwamnatin jihar mungani ya aiwatar alhamdulillahi muna godiya.

Abu na biyu da muke fatan gani shine ziyartar asibitoci mallakar gwamnati yayin rashin lafiya wannan ko shakka babu zai inganta yanayin aiki a wadannan asibitocin, tare da farfado da asibitocin daga mummunan yanayin da suke ayau.


Kamar yadda ake cigaba da gine-gine a Babban asibitin na katsina, muna fatan ganin a kammala bada jimawa ba. Sannan kuma bayan kammalawa akwai bukatar ziyarar bazata ga mai girma gwamna akai-akai badan komai ba sai don ganin anyi abinda ya dace musamman ga majiyata da kuma su kansu ma'aikatan.

No comments:

Post a Comment