JAWABIN MAIGIRMA ALH. UMAR ABDU TSAURI (TATA) A WURIN TARON KARBA TARE DA KADDAMAR DASHI DA MAGOYA BAYAN SHI CIKIN JAM’IYAR PDP. RANAR TALATA, 31/01/2017, A BABBAN DAKIN TARO NA SAKATARIYAR JAM’IYAR PDP DAKE GARIN KATSINA, A JIHAR KATSINA.
Jama’a Assalamu Alaikum!
Na farko ina godia ga Allah madaukakin Sarki da ya hada mu a wannan wuri
babba mai albarka a wannan rana ta talata. Cikin taimakon Allah yau a cikin
Jam’iyar PDP, a cikin sakatariyar PDP tare da manya manya jami’an ta. A cikin
ikon Allah yau lema ta bude gani a karkashinta nike gudanar da ayyukan taimakon
ubangiji.
Ina neman taimako a yafe mani bin protocol, wannan ba komai yasa ba sai
don ganin an dade kuma ga lokacin sallah na karatowa, don in gaggauta ko munyi
abinda ya kawo mu don mu samu muje mu bada farali.
Na farko ina son Al’umma su sani, ni da nazo wannan wuri na zo ne domin
kauna da biyayya. PDP dama cen Jam’iya tace, kuma har yanzu Jam’iya tace, koda
na tafi APGA zuciyata tana cikin PDP. Allah cikin nashi iko, yau na dawo gida,
kuma gidan ya karbe ni, ba karba kadai akayi mani ba, an kuma karrmani. Lokacin
da akayi shawarar ayi wannan taro, kwata-kwata awa 24 da suka wuce, na ce
aikuwa babu lokacin da zan shirya, in kuma sanar da al’umma ta. Amma aka ce inzo
da mutane na ko ya ya suke. To chairman ga mutane na, Allah cikin nashi iko na
kawo gare ka. Mu masoya ne, kuma ina tabbatar maka mu masu biyayya ne ga
jam’iya.
Kowa in akace Tata, abinda ake kallo shine abu biyu ; Na farko shine
za’ayi fada, Na biyu da ance Tata, za’ace Gwamna yake nema. To ni nazo nan a
matsayin mai neman sulhu. Fada in anyi shi an yishi akan kuskure kuma ya riga
ya wuce. Na biyu, naji Hajia Binta Dubai tana gabatar dani a Matsayin Dan
takarar Gwamna, a’a ni din nan nazo ne a matsayin Yaro na Jam’iyar PDP. PDP ita
keda yancin tura ni inda ya dace. Yau in PDP tace inje inyi takarar Kansila a
Dutsinma ‘A’, to gobe zanje in fara takarar kansila. Amma ina da yakinin adalai
ne akan teburin nan, sun san kansila already akwai kansila wanda suna court so
muke su dawo da kujerar su, inshaa Allah. Sun sani, already muna da chairman,
shima suna court so mukeyi kujerar shi a dawo mashi da ita. Amma kowa ya sani
Katsina bamu da Gwamna. Saboda haka anan, in yanzu cewa nayi so nike muje mu
shiga wancen gidan to dama ai mu muka gina shi. Maigirma Chairman, kamar yadda
na fada maka ni mai biyayya ne umurni nike Jira, in kace mu tafi wallahi zamu
tafi yanzu.
Nazo wannan wuri domin in gaya maku da yardar Allah Katsina sai mun karbo
ta. Katsina sai ta dawo wannan gidan da yardar Allah. Duk wanda ke wannan wurin
ya gode ma Alla, tunda suka shiga wancen gidan, sun shige shi ne a karkashin
Darajar wani, amma su basu da darajar data isa ta kaisu wancen gidan. Mu tsaye
muke da kafafunmu. Ayyukanmu sun ishe mu. Yau in akace Jihar Katsina sai ance
Umaru Musa Yar’adu (Allah ya jikanshi), to Umaru Ya tafi, Umaru ya dawo. In
akayi maganar Jihar Katsina, sai ance Ibrahim Shehu Shema, to Shema ya tafi, ga
Tata ya dawo.
In aka duba duka bangarorin guda biyu, ina da kafa gidan Umaru, ina da
kafa gidan Ibrahim. Ina mai tabbatar maku ayau da aka mika ni ga hannun
Chairman, inda ba don biyayya ba, da sai ince nafi kowa halatta a cikin
jam’iyar PDP.
Al’ummar Jam’iyarmu dake wannan wuri, aikin dake a kanmu babba ne. na
fada na maimaita, kar mu koma mu kwanta muce shirme suke yi. To in su shirme
suke yi in muka kwanta to kaga mu kwance muke. Da wanda ke tsaye yana shirme da
wanda ke kwance yana barci, ni ina ganin wanda ke tsaya yana shirmen nan ya fi
mai baccin nan. Kar mu dauka cewar nasara ajiye take kawai tashi za’ayi a dauke
ta. A’a, Allah akwai aiki a gaban mu. Yau cikin taimakon Allah, ni dai ina gaya
maku na shirya aikin nan kuma gashi na fara. Saidai ina so ku sani, shi aikin
Katsina, ba aiki bane na raggo, shi aikin Katsina, ba aiki bane ba na marowaci,
aikin Katsina ba aiki bane ba na matsoraci, kuma aikin Katsina ina mai tabbatar
maku sai mun yishi.
Yau a cikin Jihar nan, bayan Jam’iya ta PDP a Jam’iyance, nine na biyu da
mutanen nan kullum suke so suga sun wulakanta. Da kunji ance za’ayi taro a
karbi wasu mutane, cewa akeyi Jama’ar Tata ne, ni kuma Jama’ata gasu nan,
wadancen dama ba nawa bane. To na fada masu da babbar murya, in sun karbi wasu
ba Jama’ata bane, in sun karbi wasu ba yan Jam’iyar PDP bane, tarkace suka
karba, aikin banza suka karba, kuma akanshi zasu kare.
Na sha fadi, ban taba ganin mutumin kirki ba irin dan Jam’iyar PDP,
saboda PDP itace Jam’iyar dake mulki, amma kaga dan jam’iyar PDP bashi da ko
kwabo amma ya fito yayi aikin don saboda jam;iya. In akayi maganar akida,
wallahi akida tana cikin PDP, su wadancen da suke cewa su yan adawa ne, kuma
adawa tana tafiya da aqida, to ba gaskiya bane. Suna adawa ne saboda bakin
ciki. Mu kuwa yau in akace muna adawa, to muna adawa ne saboda bakin cikin
ganin halin da al’umma ta ke ciki. Kudurin mu shine, ta ina zamu bi mu tsamo
al’umma daga halaka.
Yau shekara biyu Kacal da hawan mulkin su amma komi ya canza. Ni da ana
kamfen na sayi tirelloli na shinkafa, na sayi tirelloli na taki, na sayi
tirelloli na masara mun bayar kyauta gudummuwa ga al’umma. Amma ina mai
tabbatar maku kafin wani zaben yazo, kasar nan sai an nemi wanda zai sayi
tirellar masara ya bada kyauta kasar nan an rasa. Domin ni da nasayi masara
akan naira dubu hudu(4,000) nayi kyauta da ita, yau buhun Masara yana Naira
dubu goma sha Shida (16,000). Kudin da na sayi tireller dasu, yau sai anyi da
kyar zasu sayi mani buhu 50 dasu. Ana rayuwar duniya haka?
Sun ce mu barayi ne, in ma mu barayi ne to munyi sata mai amfani, domin
mun yi satar kuma mun gina al’umma. Sun ce su basu sata shi yasa ma muke yunwa.
To kenan da gaskiyar dake kashewa, da satar dake amfanawa, wace tafi amfani ga
al’umma. Yau in gaskiyarsu tana da amfani to su take amfana, mudai bamu ga
amfaninta ba ga al’umma. Kuma wallahi har gaskiyar mun fisu. Jarabawace ta
Allah, ya karba daga garemu ya basu, kuma don ya nuna ikonshi, don ya nuna mu
wadanne iri ne, suma al’umma ta gane wadanne iri ne.
Yau suna son su kawo Ibrahim Shehu Shema a cikin Jihar Katsina don su
wulakanta shi. Yau ina son duk wanda ke wannan wuri ya sani, ana cewa Tata da
Shema ba su shiri, wanene ya fada muku? Wallahi ni ina yima shema addu’a ta
alkhairi, kuma duk inda zan tsare mutumcin shema dama na taba yi, kuma a sanya
ni kan hanya zanyi da yardar Allah.
Yau duk wanda ya wulakanta shema ai mu ya wulakanta. Ina bada hakuri da
wanda ke son shema da wanda bai son shema anan, ina so ku sani, dukkanin mu
Jam’iya ta hada mu, kuma Jam’iyar nan ayau itace rigarmu itace wandon mu, kuma
tana tafiya da wani abu da ake cema symbol, alama kenan, to alamar daukakar PDP
a jihar Katsina ba kowa bane Ibrahim Shema ne, ko anqi, ko anso maganar kenan.
To yau duk wanda ya karya Ibrahim Shema a cikin Jihar Katsina, wallahi mu aka
karya. Saboda haka duk wanda zai iya bada gudummuwa akan Allah ya hana su samun
nasara akan wannan danyen aiki, to ya bayar. PDP itace gare mu, PDP itace gaba,
kuma akan PDP inshaa Allah shirye nike inyi duk abinda ya dace. Saboda haka ni
bani gaba da kowa, bani fada da kowa, tarbiyyar gidanmu itace rungumar al’umma.
Ban taba cewa sai mai so na zan amfanar ba. Buri na shine Allah ya bani abinda
zani yi, in ya bani to zanyi, in kuma banyi ba, to bani dashi. Wallahi ban taba
kwana da kowa ba a raina. Na shigo Jam’iyar PDP don in bada gudummuwa ta samu
daukaka.
Ina so ku sani, a cikin masu taimakona, bangarori biyu ke taimako, na
farko Jam’iyar nan da nike cikinta itace ta farko dake taimako na. Wanda ke yi
mani jagoranci mai mukami ne a cikin Jam’iyar nan. Wadanda ke mani Jagoranci a
Local Government, babu inda na samu mai gudummuwa ko mai Jagoranci ba tare da
yarda ta Jam’iya ba. Ance a wancen lokacin nayi kuskure ban rungumi Jam’iya ba,
to yau gani na rungumeta.
Wanda duk zayyi magana yace Tata dan takara ne to ya sani, Tata dan PDP
ne ba dan Takara ba, Takara bata zo ba. A cikin PDP kuma Tata dole ya samu masu
Jagoranci da zasu dora shi kan hanya. To suwa zasu dora shi kan hanya inba
wadanda suka san Jam’iyar PDP ba? To ina so ku sani duk wanda yake ganin nayi
ba daidai ba akan na rungumi yan jam’iya suna Jagoranta ta a cikin jam’iya, ina
so ya gane cewa, hausawa sun ce, Sai da Dan gari akan ci gari.
Na biyu akwai Matasa dake karkashin su, matasan nan akwai kungiyoyi daban
daban, saidai a cikin su, akwai kungiyar da ake kira Tata Dawo Dawo, kungiyar
nan tana aiki tukuru tsakanin ta da Allah. Akwai wuraren da takai wanda ni ban
isa in kai ba. Saboda haka ina maku godiya Allah ya saka da Alkhairi.
Ina so Dawo Dawo ta sani, in dai dawowa ce to gani na dawo. Bance ku
canza sunan kungiya ba, amma ku sani, wannan aiki kun yishi, kuma kun dora ni
akan hanya, sannan akan hanyar nan akwai jagorori, ina rokonku kuyi masu
biyayya. Babu Jayayya tsakanin Tata Dawo Dawo da sauran kungiyoyi, da kuma
jagoranci dake karkashin Alhaji Umar Makauraci. Karkashin shi kuke, kuyi masu
biyayya, in kuka yi mashi ni kun karrama ni.
Daga karshe ina so inyi kira ga Jam’iya, mu adalci muka sani. In akayi
mana adalci wallahi duk inda ake zaton bamu iya zuwa za’a aike mu kuma zamu je.
Yau Alh. Salisu Majigiri, Allah kai yaba shugabancin Jam’iyar PDP, Saboda haka
ina so ka sani, kaine zaka tsaya gaban Allah kayi bayanin yadda kayi jagorancin
ka, babu wanda zai iya tsaya maka a matsayin lauya. Saboda haka tsakaninka ne
da Shi zaka yi.
Yau ita ce rana ta biyu dana taba haduwa da Majigiri, amma ranar dana
fara ganinshi, nayi magana dashi, sai nake mamakin don mi abubuwan da ake fada
mani basu yi daidai da mutumin dana gani ba? Akwai adawa cikin PDP yanzu haka a
Jihar Katsina. Kuma adawar nan ba komai ya jawota ba rashin fahimta ne. Babu
dalilin da zai sanya ace yanzu muna court saboda shugabancin Jam’iya. Shi dai
shugabanci Allah ke bada shi ba alkali ba. Yau in ka kwace shugabanci daga
hannu Majigiri wa zaka ba? Shi zabi Allah ake barwa shi, ba tilas ake yin zabi
ba. Majigiri Allah ya zabe shi, to mu kuwa yi mashi biyayya. In ka cire
Majigiri ba mu san cikin rikincin da za a sanya mu ba. Saboda haka Maigirma
Chairman, nazo ina yi maka biyayya, kuma zan taimakeka akan wannan shugabanci
da kake yi.
Ku kuma sauran Al’umma ina so ku sani, in kun shirya fada to gani, saidai
wannan fadan ina tabbatar maku mai zafi ne. Yau a Jihar Katsina bamu da ko
Councilor. Zamu tunkari Gwamnatin da ita keda sama, kuma ita keda Jiha, duk
wani mukami da ake nema yana hannunsu. To a siyasa abinda aka koya mani, wanda
duk keda Gwamnati ya tsera maka a wurin zabe. Saboda haka wannan aiki ne babba
sai mun dage. Ni dai ina shaida maku wallahi na shirya.
Da duniya nike so baku gani na nan. An bani Minister don in bisu nace
bani so, an bani Deputy Governor tun ina takara nace wallahi gwara a bani
C-Class, saboda baiyi daidai da abinda nike bukata ba. Ni so nike in kai ga
al’umma in taimake ta. Ba wurin boyo nike nema ba don in sami abinda zan sa
aljihu. Talauci da Arziki duk na Allah ne. Yau idan na rasa na barwa Allah.
Banzo nan don in yaudari wani ba. Buri na shine ta ina zan taimaki Addinin
Allah ya sami gata, ta ina zan kawo gudummuwa ga talaka har ya samu saukin
rayuwa.
Ba zan taba neman Gwamna ba sai in kun ce, duk ranar da kuka ce in fito,
to zan fito, amma ba zan iya ba sai kun taimake ni. Ni kadai bani iyawa. Amma
da yardar Allah in muka hadu, zamu kai duk inda ba’a zato.
Ina godiya ga manyan baki, ina godiya ga jam’iya data karrama ni. Ina
rokon yadda Allah ya hada mu anan, Allah ya sake hada mu a gidan gwamnati 2019
inshaa Allah.
Na gode kwarai Allah ya saka da alkhairi.
No comments:
Post a Comment