Friday, 19 October 2018

Bambamcin Aya Da Tsakuwa- Nuraddeen Adam Tina


Mafi yawan al'umma suna mamakin yadda Hon. Umar Tata tare da yan koral din sa ke cewa Gwamna Masari yafi Senator Yakubu Garba Lado Danmarke chanchanta, wannan shine dalilin Komawar Hon. Umar Tata APC kunga kenan ko anan sun nunawa jama'a cewa ba saboda cigaban al'umma suka koma APC Ba, Sun koma ne saboda son zuciyar su.

Idan jama'a Zasuyi duba da matsayin da Gwamna Masari ya rike kafin yayi Gwamna zaku ga cewa Senator Yakubu bai rike shi ba, tunda yayi Kwamishinan ruwa daya rike har zuwa Majalisar tarayyar Abuja har ya zama speaker idan kaje Kafur ba zaka iske mutum Ukku wanda Gwamna Masari ya samar ma aiki ba, Kaga Kenan idan har mutum zai rike muƙami na Ukku a Nigeria ya gaza samarwa dangin sa aiki ai kaga baka hada su da wani mutum mai daraja ba kwatankwacin Senator Yakubu Danmarke ba.
Babu wani aiki da DG Tata zai nuna a Masari Ward wanda akayi lokacin da masari yake na Ukku a Kasar Nan.
An zabi Masari a matsayin dan majalisa mai wakiltar Malumfashi/Kafur, haka aka gama Wakilcin majalisar tsawon shekaru 4 Babu ko tsarabar Abuja ga al'ummar wannan yanki.
Haka kuma Gwamna Masari ya samu sa'ar yin tazarcen kuma cikin ikon Allah aka zaɓe shi Speaker na Nigeria, amma a hakan al'ummar yankin Malumfashi/Kafur kai harma da jihar katsina suna ɗoki suna murna nasu ya samu Zaa kawo aikace-aikacen raya kasa da inganta rayuwar mazauna jihar nan dama wajen jihar nan baki daya.
Amma mamadin mu samu cigaba sai muma samu akasin haka, duk jama'a suka maida wukar su a bakin kube, domin basu ga wani aikin azo a gani da yayi ba.
An yi speaker kala daban daban a Nigeria, tun daga mulkin Demukuradiya har zuwa yanzun duk wanda ya rike speaker na kasa yana da abun nunawa a jihar su, amma Gwamna Masari baya dashi, idan kuma yana dashi sai a fili a faɗa mana shi ina jiran DG Tata dan tallar Masari ya nuna mana shi koda a kafar sadarwar Facebook Ce.
Kowa Yasan Guguwa ta kawo majority ɗin masu mulkin yanzun musamman Rt. Aminu Masari wanda DG Tata yake tallata hajar sa.
Cikin ikon Allah yanzun anyi ruwa Guguwa ta daddale, babu sauran Guguwa a kakar zaɓe ta 2019 da yardar Allah, chanchanta Zaa duba ba Sak ba.
Lokacin da Gwamna Masari yazo Katsina komai yana tafiya daidai dukkan al'amurran jihar nan suna tafiya akan layi babu saɓa number, amma yanzun a Kasar nan jihar katsina tana daga cikin koma baya a Kasar Nan duk dan saboda irin rikon sakainar kashin da Gwamna Masari yayi mata.
Shekarun mu Ukku kenan muna gab da shiga ta Huɗu, amma har yau babu abunda DG Tata zai iya nunawa na Masari wanda ya wuce rashin tsaro, talauci da tada hankalin al'umma, sai kuma shegiyar abunda ta addabi al'umma wato YUNWA, wanda kai kanka kasan ana yunwa shiyasa ma kaida kanka ka Kirkiri Shirin "A KORI YUNWA" amma mamadin kaika kori yunwa, sai gashi ita YUNWAR TA KORE KA, ɓuge da tallar dan takara akan million GOMA 10,00000.
Kamar yadda Hon. Umar Tata ko ince DG Tata ya faɗi a wani taro da akayi wajen amsar Mustapha Radda, cewa al'umma su tashi tsaye wajen karatun maganar karatun yayayen su da masari ya gaza biya masu kudin waec/neco, Hakan ne ya tabbatar da gazawar APC tun a wannan lokacin har yanzun gaskiya kara bayyana take a fili ta fuska daban daban, Hakan yana nuni da cewa Insha Allahu Mune keda nasara kamar yadda na hannun damar ka Mustapha Radda ya fadi cewa zaben 2019 PDP zata lashe shi, Dukkan Alamu sun tabbata na faɗuwar zaben APC.
kullum babu wani Aiki daya wuce tura al'umma gidan radiyo da telebishin da jaridu, domin a kare alkawarin da akayi aka kasa cikawa.
Kowa Yasan cewa wannan gwamnatin babu abunda ta Chanza sai maida na cikin inuwa a rana, maida na haske zuwa duhu, yuwan zuwa koshi da dai sauran su.
A 2015 babu yadda engr. Musa Nashuni saida yace ma al'umma cewa kada su jama'a su Kuskura su Chanza ilimi da ake ba yaran su kyauta ko kuma albashi da ake biya akan lokaci. Bayan an Zaɓi gwamnatin APC kuma engr. Musa Nashuni yace daman saida na faɗi maku cewa kada ku Chanza ayyukan Alkhairin da Gwamna Shema yayi, amma saboda an rude ku da rokon baka kuka chanxa, to gashi magana ta ta tabbata inji engr Musa Nashuni.
Daga karshe ina son DG Umar Tata ya sani jihar katsina bata bukatar Gwamna Masari kuma da yardar Allah zamu amshi jihar nan a 2019.
Allah ya bamu ikon Korar Yunwa a kakar Zabe ta 2019 kamar yadda Hon. Umar Tata yake fata a baya kafin ya chanza ra'ayin sa akan kudin tada koma ɗa da babban Attajiri ya bashi.

Nagode. Nuraddeen 
Adam Kankara Chairman 
SMO.


No comments:

Post a Comment