Monday, 24 September 2018

Katsina PDP na cikin hadari,alamu na nuna cewa za su iya rasa Umar Tata


Alamu na nuna cewa Umar Abdullahi Tsauri zai koma jam’iyar APC a jihar Katsina bisa rashin zama dan takarar kujerar gwamnan jihar Katsina.
A yau jam’iyar PDP reshen jihar Katsina ta saida Senator Yakubu Lado Danmarke a matsayin dan takarar ta na kujerar gwamna bayan yar gajeruwar zabe daya gudana.

A binciken Cliqq Magazine Hausa ta gano cewa akwai yan takara irin su Ahmed Aminu Yar’adua da suka ki amincewa da salon da aka bi wajen yin zaben.
Amma magoya bayan Umar TATA tuni suka fara ficewa daga jam’iyar PDP da yin Allah wadarai da rashin yin adalci ga yadda shuwagabannin jam’iyar su kayi.
Daga cikin yaran TATA da suka fita akwai Abdul Danja wanda shine mai taimaka mashi wajen sarrafa hanyoyin sadarwa na zamani.
Abdul ya baiyana ma Cliqq Magazine Hausa cewa lallai shi ya fita daga PDP kuma yana fatan ubangidan sa Umar TATA ma zai fice daga PDP.
Fitowar Senator Yakubu Lado a matsayin dan takara ba abun mamaki bane ganin yadda aka dade ana rade radin cewa tsohon gwamnan Katsina Ibrahim Shema ya hakikance akan dole sai Yakubu Lado.
Wata majiya mai karfi ta shaidama ma wakilin mu cewa, a zaman da yan’takarar suka yi a satin da ya gabata, sun amince akan azo ayi zaben fidda gwani da sharudda akan cewa baza ayi amfani da kudi ba musamman ma wajen sayen daligat, amma wasu nazargin Yakubu lado da amfani da kudi ta bayen fage.
Amma yanzu alamu na nuna cewa Umar Tata zai koma APC ganin  irin rashin adalci da PDP tayi, amma wata majiyar daga gidan TATA sun baiyana ma wakilin mu cewa zasu dan saurara har zuwa sati daya kafin su fitar da sanarwar jam'iyar da zasu koma.
Tabbas PDP a Jihar Katsina ta tsunci kanta cikin wani hali mai wuyan sha’ani musamman ma yadda talakan Katsina yake tsammani zasu kamanta adalshi, tambaya anan shine, mene ne mafita ga irinsu Umar TATA da sauran yan takarar?



No comments:

Post a Comment