Thursday, 28 September 2017

Takaicin Maza Ne Ke Sanya Matan Katsina Shiga Shaye Shaye – Saulawa

Takaicin maza ne ke sanya matan Katsina shiga shaye shaye – Saulawa

- Wata matashiya ta bayyana dalilin da yasa mata ke shiga harkar shaye-shaye a jihar Katsina 

- A cewarta takaicin maza ke haddasa hakan 

- Saulawa tace idan ba’a shawo kan wannan matsala cikin gaggawa ba, za’a samu karin tabarbarewa tarbiya 


Wata matashiya a jihar Katsina da aka ambata da suna Khadija Saulawa ta bayyana yadda takaicin maza ke sanya matan jihar shaye-shaye. 


Saulawa, ma'assashiyar wata kungiya mai zaman kanta ‘Queen Dijah Women and Children Awareness Initiative’ tace kudirin ta shine ta wayar da kawunan mata akan illolin dake tattare da wannan harka. 

A wata zantawa da tayi da jaridar Vanguard, Saulawa tace idan ba’a shawo kan wannan matsala cikin gaggawa ba, za’a samu karin tabarbarewa tarbiya a nan gaba. 

Saboda a cewar ta “Idan kullum uwa na cikin maye wa zai kula da yara?” 



Ta ce yawanci mata na shiga harkar shaye-shaye ne da zaran an fada masu cewa zai kawar masu da bakin cikin da mazajen su suka sanya su a ciki. 

Ta ce da sun dandana suka ji dadi, shikenan ba za su iya dainawa ba.

Saulawa ta kuma ce kungiyar ta ta za ta mayar da hankali a bangaren fyaden kananan yara, wanda ta ce shi ma ya zama ruwan dare a Katsina da samar da tsaftataccen ruwan sha. 

 Ku same mu a www.facebook.com/Cliqq.Magazine

Ko Whatsapp @ 07032183026

No comments:

Post a Comment