Thursday, 28 September 2017

FUNTUA: Da Yiyuwar In Tsaya Takara a Zaben 2019 - Zainab Ghana



Image may contain: 1 person, smiling, closeup


- Shahararriyar yar siyasar nan da ta fito daga karamar hukumar Funtua a jihar Katsina, Hajiya Zainab Ghana ta bayyana cewa akwai yiyuwar ta tsaya takarar majalisar garin na Funtua a zabe mai zuwa.

- Zainab Ghana wacce ta bada gagarumar gudunmowa wajen kafa jam’iyyar APC a Katsina dama kasa baki daya ta ce Al’umma na yawan kiranka akan ta tsaya takara.

- A cewar Zainab Ghana, Kiraye Kirayen Al’ummar karamar hukumar Funtua na nuni da cewa Mazan da suke wakiltarsu sun kaa biya masu bukatunsu, don haka akwai bukatar baiwa mata dama don suma su taka irin tasu rawar.

A zantawar tad a wakilin ClIQQ Magazine ta wayar salula, Hajiya Zainab Ghana ta bayyana wa Sani Hamza Funtua dalilan da ka iya tilasta mata fitowa takarar majalisa don wakiltar Funtua a majalisar dokoki ta jihar a zabe mai zuwa.

Da farko ban taba kawo ma raina cewa zan tsaya takara ba, har zuwa yanzu da nike Magana dakai ban yanke hukunci akan kiraye kirayen mutane na in fito takara ba, amma ba wai hakan na nufin b azan fito takarar ba.

“A kowace rana idan nah au kafafen sada zumunta na zamani musamman ma irinsu Facebook da Whatsapp, nakan ci karo da sakunan mutane da yawa na cewa in zo in wakilce su a matakin jiha. Hakan ke sa ni tunanin cewa watakila saboda mazan sun kasa cika masu alkawuran da suka daukar masu ne yasa suke so na fito takara”


Hajiya Zainab Ghana dai ta dade tana gwagwarmaya don ganin cewa karamar hukumar Funtua taci gaba, kamar yadda tace:

Ni yar siyasa ce, bani da wani buri day a wuce inga karamar hukumar Funtua taci gaba, musamman ma idan muka duba irin matsalolin da garin ke fuskanta.

“Har zuwa yanzu, an maida mata shanun ware a dukkanin wasu sha’anoni na siyasa ko tallafi, kuma sune ake neman kuri’arsu idan zabe yazo, amma da zaran zabe ya wuce, shi kenan an maida su ba a bakin komai ba. Ina da burin ganin cewa Mata sun ci gajiyar romon demokaradiya, ina so inga cewa zaman banza a tsakanin matasanmu ya kare.

“Matsalolin da Funtua ke fuskanta sun hada da rashin ababen more rayuwa, rashiin aikinyi a tsakanin matasa, rashin bada tallafi na karatu ko kuma koyar da al’umma sana’o’in hannu, uwa uba maida matasa yan bangar siyasa.”

Hajiya Zainab, Ta bayyana cewa, idan har ta samu dama, zata tabbatar da cewa Karamar Hukumar Funtua ta zamo zakaran gwajin dafi a kananan hukumomin jihar Katsina.

Daga Karshe tayii kira ga dukkanin mutanen dake yi mata fatan alkairi da kuma son ta fito takara dasuyi hakuri, idan hart a yanke shawara kan hakan, babu abinda zai hanata fitowa.

Ga wadanda ke kirana ta waya, ko aika min da sako ta yanar gizo, ina godiya kuma ina kan tunani akan wannan kira nasu, tabbas b azan zura idanu in kyale Funtua taci gaba da tafiya cikin duhu ba, idan har na shirya, to zan sanar wa al’umma hukuncin dana yanke.”

Wannan dai shine kusan karo na farko tun kafa karamar hukumar Funtua, inda al’umma ke neman mace ta tsaya takarar majalisa don wakiltarsu a matakin jiha, wannan kuma na daya daga cikin nasarar demokaradiya na baiwa ko wane jinsi dammar yin zabe ko tsaya takara don a zabe shi.


Daga Teburin Edita: Sani Hamza Funtua
Whatsapp Only @ 07032183026

No comments:

Post a Comment