Wednesday, 8 March 2017

Tsokachi Da Sharhi Akan Gwamnatin Jahar Katsina Daga Muhammed Aminu Kabir


Da Farko dai dole in danyi waiwaye akan yadda wannan gwamnatin tazo inyi matashiya da irin halinda Al-umma ta tsinchi kanta a ciki.

Kafin zuwan wannan Gwamnatin wata gwamnatinche akai wadda Al-umma suka dora ko aka doramasu ta hanyar yin zabe, tundaga shekarar da aka koma mulkin damakaradiyya a nigeria Jamiyyar PDP ce take mulki a Jahr Katsina har zuwa Shekarar Dubu Biyu da Sha Biyar inda Al-umma tayi tashin Farin Dango daga wac...cen Jamiyyar zuwa Jamiyya mai Mulki a Yanzu wato APC.

Bazamu yi Butulchiba wajen Fadin cewa Jamiyyar data gabata takawo cigaba a Jahar Katsina a Fannoni daban daban duk kuwa da cewa akwai zarge zarge na yin Al-mundahana da Dukiyar Al-umma nan da chan, amma haka bazaisa mu rufe Ido muche Jamiyyar batayi komai ba, akwai kura kurai da sukayi wanda suka sa Jamaa suka kaurache masu lokacin zabe suka zabi Jamiyya mai Mulki a Yau.

To da alama itama Jamiyyar mai Mulki tana kan hanyar maimaita wasu daga cikin irin Abubuwan da suka sa aka kaurachema waccen gwamnatin aka zabeta.

Gwamna da Masu taiamakamasa a harkar Mulkin Jamaa.

Idan mukayi duba da yadda gwamnati take tafiya zamu ga cewa Shi gwamna yanada kishin yaga yayima Al-ummar Jahar Katsina Aiki to amma wasu daga cikin masu taimakamasa lallai kamar sunayi masa zagon kasa ne basa son ganin gwamnatinsa tacigaba kansu kawai suka sani da Iyalansu basu da niyyar kawo sauyi a tafiyar wannan gwamnatin.

Your Excellency Shawarata a wurinka shine lokaci yayi da zakayi sauye sauye wato garambawul a cikin gwamnatinka nasan kana da rahotanni kala kala daga bangarori daban daban na irin yadda ake ma tafiyarka zagon kasa, to karka duba kowa ka duba Jahar Katsina duk wanda baya nan sirri suka nuna cewa baya kishin Al-umma kansa yasani to ayi kakkaba kowa yagane inda dare yayi masa.

Al-umma basu da shakku akanka to amma kasani cewa duk wani abu da akayi Mai kyau ko akasin Haka kai ake kallo ba masu taimaka maka ba, Allah yabaka ikon sauke nauyi da yake kanka Amin.

Muhammed Aminu Kabir

Wannan rubutu ba ra’ayin Cliqq Magazine Hausa bane illa iyaka na shi marubucin da ya rubuta. Cliqq Magazine ba ta da hannu a cikin wannan rubutu kuma da kuma duk abun da zai biyu baya.

 

No comments:

Post a Comment