Wednesday, 8 March 2017

BUDADDDIYAR WASIKA ZUWAGA SANATA MAI WAKILTAR KATSINA TA TSAKIYA DA DANMAJALISA MAI WAKILTAR KARAMAR HUKUMAR KATSINA DAGA Mubarak Jibril


Ina ma farawa da yi maku sallama irin wadda addinin musulunci yayi tanadi tare fatan wannan wasika zata isheku cikin kushin lafiya, ina kuma fatan zaku kalli wannan wasika tawa da idon basira ba don komi ba sai don muhimmanci da nike ganin tana dashi musamman gas u wadanda na rubutu wannan wasika domin ceto rayuwar su.


Ita dai wannan budaddiyar wasiqa na rubuto ta ne domin rokama yaran mu wadanda ke shekarar karshe ta makarantun sakandire na jihar nan da basu samu dammar cin jarabawar sharefage da ke bada dama gwamnati ta biya masu kudin jarabarawar kamala karatu sakandire (SSCE) Alfarmar da ku taimaki rayuwar su, ku biya masu kudin jarabawar nan duk da dai a halin da ake cikin yanzu kusan an gama da jarabawar WAEC an fara karbar kudaden jarabawar NECO su samu suyi koda NECO din ne wallahi wannan jarabawar tana da matuqar muhimmanci a rayuwar su, zata iya zama sila da wani daga cikin su ya samu damar da zai iya wuce wa makaranta ta gaba domin karo karatu har ya zaman ma al’umma abun alfahari.

Sbiya masu kudin jarabawar nan kamr sadaka ce mai gudana domin kuwa duk al’fanun da aka samu ta hanyar wannan jarabawa wallahi kuna da lada, kunga kenan kun taimake su kun taimaki rayuwar su, kuma kun taimaki iyayen su ita kanta al’umma ai taimaka mata wajen rage yawan bata garin yara a cikin gari. Na tabbatar kun san muhimmmanci da ke akwai a tattare da yin karatu, kun san ribar da ake samu acikin yin karatu kuma kun sani cewa a irin wannan zamani da muke cikin babu abinda zaka yi ma mutum wanda yafi ka taimaka mashi ya yi karatu duba da yanda karatun ya zama shine akan gaba wajen komi day a shafi al’ummar wannan zamani.

Duk yanda wani yake so ya taimake su anan gaba madamar basu yi karatu ba fa to babu abinda zai iya yi masu illa ya basu naira dari ko dari biyu wanda baza ta ma ishsu ba ko su ci abincin rana guda, kuma na tabbata har ga Allah ko anan gaba a rayuwa duk wanda kuka taimaka har ya samu damar yin karatu ba zai taba mantawa da ku ba har acikin addu’o’in shi. Duk yanda iyayen yaran nan suke so su biya masu kudin jarabawar nan basu da hali, kokarin su ma suga sun sama masu abincin dasu ci yau da gobe ba kudin jarabawar ba.

Akwai takaici ace yara sun share shekara shida suna zuwa makaranta amma anyi masu wannan jarabawa ta share fage (Qualifying Exam) amma sun fadi sai dai kuma yafi zama abin takaici idan akace wadan nan shekaru shidda sunyi su ne amma hakanan zasu tafi ko takardar tsire ba a basu ba (ba testimonial balle results) babu wata takarda da zata nuwa cewa sunje makarantar babbadr sakandire. Kuma tabbas wannan ka iya zama barazana ga al’umma domin kuwa mayi yawan wadanda ke ba al’ummar mu matsala sune irin wadanda basu kamala karatun sakandire ba.

Ina fatan zaku yi amfani da damar da Allah ya baku domin cewa wadannan bayin Allah da al’umma baki daya domin biya masu kudin jarabawar nan.

Comrade Mubarak Jibril Yankyaure

talk2yankyaure@yahoo.com

Wannan rubutu ba ra’ayin Cliqq Magazine Hausa bane illa iyaka na shi marubucin da ya rubuta. Cliqq Magazine ba ta da hannu a cikin wannan rubutu kuma da kuma duk abun da zai biyu baya.

No comments:

Post a Comment