Friday, 3 March 2017

Karanta Cikkaken Bayani Akan Bugun Da Malami a KCK Yayi Ma Wata Daliba Amina-Gaskiyar Magana

Amina Bishir
Labarin wata yarinya yar’makaranta wadda ta ke karatu a Makarantar Sakandare ta Katsina College Katsina wadda ta samu matsala wajen Karatun ta domin wani malami da yace tayi mashi dariya, wanda tace baza tayi ba, wanda yajaza mata bugu wanda malamin Makarantar yayi mata har iyayenta suka nuna bashin ransu, daga bisani kuma sai aka dakatar da ita daga zuwa makaranta.

Cliqqmagazinehausa.com tayi tattaki zuwa wajen ita yarinyar/dalibar da kuma Makarantar su yarinyar domin jin gaskiyar abun da ya faru.

Amina Bishir sunanta kuma dalibace a Katsina College Katsina wanda yanzu haka ajin ta ukku (SS3 Art 5) ta baiyanama wakilin jaridar Cliqqmagazinehausa.com yadda abun ya faru kamar haka

“Ina cikin aji ina rubutu, sai Mallam ya shigo wanda aka fisani da ‘Daddy’, shi Daddy ba Malamin mu bane amma ya kasance shi ke duti a ranar da abun ya faro. Ya same ni ina yin rubutu na darasin tarihi [history], ya tambaye ni me nake yi wanda nace masa rubutu nake yi, sai ya ce ma kawata ta goge jan baki da tasa. Ya juya ya tafi kenan, sai ya ce mani na kalli ita kawata dake kusa dani nayi mata dariya, wanda nace masa ni bazanyi ba gaskiya.

Sai ya umurce ni da na tashi na fita waje na tsugunna [kneel down], Kafin nafita daga cikin ajin sai ya fara buguna da bulala ta dorina, har na sauka kasa yana buguna, Allah yasa akwai ma’aikatan ma’aikatar ilimi sun zo tanttan cewa da suke yi, wanda daya daga cikin mutanen ya ce mashi ya zaka rika bugun diya mace haka da bulala, da dai suka ga ya ki barin buguna, sai suka karbi bulalan daga hannun shi. Duk da haka sai ya cire takalminshi yashi gaba da kwada mani shi akan kaina. Dana ga baya da alamar barin buguna sai nace mashi wallahi idan bai bar buguna zan gayawa iyayena domin su biman hakkina. Sai yace dani inje ‘yan gayama duk wanda zan gayamawa.

Ciwo Da Malamin ya Jimata Saboda Bugun da yamata

Ciwo da tabo kenan na bugu a hannun Amina sakamakon bugun da malami yamata
Sai wasu Malamai suka ce natafi oficin Principal domin asasanta maganan tsakanin mu. Da Pmuka je wajen Principal sai yace ma principal wai yace nayi rubutu nace bazanyi ba [alhali kuma bashi ke koya mana ba]. Sai nace bahaka abun yafaru ba wanda principal yasa aka kira shugabar ajinmu [Class captain] don tazu ta bada shaida. Da tazu sai ta zaiyana ma Principal duka abun da faru kamar yadda na bada nawa labarin yadda abun ya faru.

Kwatsam sai Mallamin yace shi wallahu sharri ne/Kazafi ne ake mashi, ma’ana da maganata da ta shugaban ajin tamu ba gaskiya bane.”

Da wakilin Cliqqmagazinehausa.com ya tambaye ta ko mai yasa bata je makaranta ba “sai tace ai an dakatar da ita sai ranar litinin aka ce ta dawo makaranta”.

Daga karshe ta jaddada mana cewa ba it aba ne ta shafa janbaki ba, kawarta tace wadda take zaune kusa da ita tashafa. Sannan kuma tace duk ‘yan ajinsu zasuyi shaidan abun da ya faru.
Tabon Bugu a kafadun hannuta kenan

Da kuma wakilmu ya ziyarci Makarantar su Amina domin jin nasu bayanin akan abun da ya faru. Cliqqmagazinehausa.com ta samu tattaunawa da maitamakin shugaban Makarantar [Vice Principal Administration] Mal. Musa Makudawa yayi bayani kamar haka;

“Abun da yafaru tsakanin dalibarmu da kuma malamin mu watau Mallam Daddy abu ne wanda duk mai kishin ilimi da kuma koyama yara dalibai da’a dole ya kyamace abun da Amina Bishir tayi. A bisa bincike da muka yi karkashin kwamitin horaswa [discipline committee] ya nuna cewa Shi Malamin ya kasance shi ke duti a Makarantar, sannan ya shiga ajin su Amina sai yaga tasaka jan baki wanda kuma a dokar makaranta bai kamata tasaka ba, kaga tun a nan ta saba ma dokar makaranta, sai ya umurce ta data goge shi sannan kuma ta juya ta kalli dalibar kusa da ita tayi mata murmushi don taga tabbas ko jan bakin ya fita, ya juya kenan zai tafi sai yaji Amina tace ubanwa zai goge, bazan goge ba. Kalmar zagin tayi mashi ya bata mashi rai har yadauki matakin bugunta da bulala.

Sannan ‘yan kwamitin Horaswa sun kira ta kuma ta amsa laifin ta har suka mata fada suka jamata kunne da kada ta sake aikata wannan abu da tayi”.

Da wakilin mu ya tambaye shi ko makaranta ta dakatar da Amina daga zuwa aji sai yace mani “Makaranta bata daka tarda ita ba amma sun kira ta sun bata takardar gaiyatar mahaifinta domin yazu makarata.”

Mallam Musa yace Baban ta bai samu damar zuwa ba sai dai Yayanta wanda ya wakilci baban. Kuma ya ba hukumar makaranta hakuri akan rashin kunya da kanwarsa tayi ma Malamin.

To kunji abun da yafaru tsakanin Daliba Amina Bishir da mallaminta Daddy. Shin ko ya gaskiyan maganar zata kaya, wannan kuma sai mun samu shaidu ‘yan ajinsu Amina Domin mu ji ta bakin su.

Yanzu Haka Amina bata san sakamakon ta ba gashi kuma har ta zu baban aji na Ukku (SS3) wanda daga shi ta kamala makaranta.

Amma kuma Mal. Musa Makudawa ya ambaci cewa Amina ba zaman da ake bada makarantarsu ba tayi rijistar jarabawa, Kenan Amina ba Daliba bace a Katsina College Katsina ga yarda yake nufi kenan.

 

3 comments:

  1. Bisa GA dukka alamu akwai zalunci cikin wannan bayani, ayi kokarin zantawa dasu bakin da suka kawo ziyara na ma'aikatar ilimi sannan yan ajinsu dalibar. Na samu shakku ne bisaga korafe korafe da nake samu ga dalibai na cikin jihar nan.

    ReplyDelete
  2. Kai, wannan abin da salka salka a cikin wannan sha'anin.
    Ya kamata a nada kwamiti mai zaman kan shi, domin a gano gaskiyar abinda ya faru. Ni kam ra'ayi na kenan.

    ReplyDelete