Cliqqmagazinehausa.com ta samu labarin wannan abun takaici daga shafin Abdullahi Hassan na Facebook. Amma tabbacin labarin bai ida samuwa ba har lokacin buga wannan wasika da mai rubutun ya rubuta a shafin shi. Amma wakillamu na iya kar Kokarin bin ciko wannan lamari don yin gaskiya ga wanda aka zalunta.
BUDADDIYAR WASIKA ZUWA GA KWAMISHINIYAR ILIMI TA JIHAR KATSINA.
Prof. Halimatu Sa'adiya.
Assalamu Alaikum,
Gaisuwa da fatan alheri gareki ya maigirma kwamishina hakika ina
cike da damuwa da takaici yanda ake gudanar da harkar ilimi a jihar nan
musamman bangaren tarbiyya tsakanin malamai da dalibai, Kokena gareki da
shawara ga wani abu da yafaru a makarantar KATSINA COLLEGE KATSINA SENIOR
SECTION (FEMALE) wadda yanzu suke da matsugunni a GOVERNMENT COLLEGE KATSINA
tsakanin 12:30pm-5:30pm tsakanin wani malami da aka boye mana hakikanin sunan
sa saidai laqabinsa MALAM DADY (CHEMISTRY) da wata daliba mai suna AMINA BISHIR
(SS3 ART 5).
ABINDA YAFARU.
Jiya talata 28/02/2017 malami mai lakabi da Malam Daddy yashiga ajinsu
lokacin da malaminsu na history yake masu darasi ya zagaya don ya duba masu
note da wadanda basuyi yana bugun wadanda basuyi ita kuma kamar yadda aka samu
shaidar ta ya isketa tanayi amma duk da haka ya nemi janta da wasa wai don yaga
fuskar ta a daure shine ya umurci ce data yima ta kusada da ita dariya wadda
ita batayin note din bayan ya bigeta, Ita kuma batayi ba wannan yajaza ya fiddo
ta ya dinga bugunta da bulala bayan malamin da yake koyamasu ya rike sa yana
bashi hakuri yasa takalminsa yadinga bugunta wanda yajaza yaimata bugun da ya
wuce wuri a fahimta ta Inda ya farfasa mata jiki.
Bayan dowowar ta gida iyayenta sukaga irin bugun da yaima diyarsu
suka garzayya da wakilinsu zuwa makarantar don jin gaskiyar abinda yafaru
saboda kauce ma jita jitar yaron zamani wanda nine wanda na take ma yayan
yarinyar baya shugaban makarantar ya amshe mu cikin mutunci da girmamawa kuma
ya aika aka kirata donjin daga gareta yaji Inda ya mika case din ga
mataimakansa mace da namiji don yin bincike agane gaskiya amma Kass Allah bai
hure masa abokan aiki ba wadanda basu san ya zasu saurari mai korafi ba suka
hau mu da fada amma dai muka matsa a bincika aka kuma bincika tare da shaidu
abinda ta shaidama iyayenta gaskia ne a cikin Shawarwarin da aka basu na
Baikamata ace malami ya tsaya wasa da dalibansa ba wanda haka ke jaza raini a
tsakani kuma bamu sani ba ko akwai wata doka data bada damar malami yace dole
sai dalibi ko daliba taimasu dariya a matsayin su na abin koyi ga dalibai hakan
baidace ba, Nasan wajibi ne dalibi ko daliba data ko ya Saba doka ta aji,
makaranta, ko hukumar ilimi dole a hukunta shi ko dan wanene amma sabanin haka
badaidai bane amma mutanen nan V. C Adm & V. C Acad suka rasa fuskar dazasu
yimana magana Mai dadi koda yarinyar ce Keda laifi abinda ake cema manner of
approaching hakan yajaza hayaniya tsakanin mu dasu, Abinda na fahimta wasu
makarantun suna da wani tsari na rashin amsar kuskuren maaikatansu da amsar
shawara da ake basu inko basu amsar shawara banga dalilin yin kungiyar iyaye da
malamai.
RASHIN SANIN MAKAMAR AIKI.
Wasu daga cikin abubuwan da wadannan mutanen suka aikata :
1.Rashin saurarar mai koke in yazo dashi.
2.Rashin iya maida ma mai koke magana.
3.Kokarin boye laifin malami.
4.Rashin tsawata ma malaman musamman matasa Masu karancin Shekaru.
1.Rashin saurarar mai koke in yazo dashi.
2.Rashin iya maida ma mai koke magana.
3.Kokarin boye laifin malami.
4.Rashin tsawata ma malaman musamman matasa Masu karancin Shekaru.
KIRAN MU AMAMADIN IYAYEN YARINYA.
Yazama wajibi hukumar ilimi tayi bincike kar ta yi amfani da
abinda muka fadi don hukunta mai laifi kowaye yin hakan shine adalci adalci
kuma na dawamar da shugabanci yai nasara yasa daukaka tunda hukumar makaranta
wakilan ta basu da manner of approach, yakamata ayi gyara bangaren malamai
musamman matasan malamai Masu karancin shekaru wajen yanda suke mu'ammulah da
dalibansu musamman mata abune kowa ya sani irin yanda abin ke gudana babu dadin
ji inba diyar ka akwai kanwar ka a cikin makarantun nasan kunaji labarin yanda
rashin kamun kai da natsuwa ke wakana tsakanin malaman matasa da daliban
musamman mata inba kaji ba ko gani ka ziyarci wata makarantar gwamnati kagani
abun akwai gyara bangaren tarbiyya wanda mafi akasarin daliban dama suna zuwa
da tasu rashin tarbiyya amma inbasuga fuska ko kofa ba to lamarin zaizo da
sauki amma da dama wasu malaman suke bude ma dalibi ko daliba kofa kodai adinga
jansu da wasa ko ace ana son su ko wata mu'ammulah ta banza su shiga tsakanin
malami da Dalibai hakan najaza raini da lalacewar tarbiya amma duk malamin da
ya kama kansa to bazai ga raini ba, inma ta rainashi to yanada da damar hukunta
ta Shima hukunci asan wanda zaiyi kar abun ya wuce waje saboda wani hukunci
yana wuce waje musamman mata.
Lallai yakamata maaikatar ilimi ta waiwaiyi wannan matsalar don
kafa doka da daukar mataki Don inhar zaasa ido a kyale to wani inyayi hakuri
wani bazai ba hakan na iya jaza daukar doka ga hannu wanda hakan zai haifar da
matsala cikin alummar mu, Kuma Yakamata a kara baiwa wasu malamai horo na
musamman bangaren yanda suyi mu'ammulah da dalibansu a makaranta da wajenta Don
gaskiya mu'ammulah akwai gyara sosai sannan iyayen yara su zage damtse wajen
baiwa yayansu tarbiyya mai kyau kuma da nuna masu mahimmancin malami ga
alummah.
Akarshe muna fatan maigirma kwamishiniyya zata duba wannan lamari
da kyau don kaucema abinda zai biyo baya da kuma rushe harkar ilimi a jihar.
Kihuta lafiya.
Abdullahi Hassan Katsina.
Abdullahi Hassan Katsina.
Gaskiya yakamata Commissioner Ilimi ta binciki ainahin gaskiyar AL'amari domin tabbatar da gaskiya. Malami: malami ne. Dalibi: Dalibi ne.
ReplyDeletewannan Magana gaskiya ce domi dukkanin nasara tana tare da gaskiya
ReplyDeletewannan Magana gaskiya ce domi dukkanin nasara tana tare da gaskiya
ReplyDeleteA gaskiya abun adubane.
ReplyDeleteAn biyashi albashi a ranar kuwa? Wlhy malamai mutane ne Kamar kowa, sunada bukatu da matsalolin rayuwa kamar kowa. Ina bada shawara ga shugabanni don Allah su duba matsalar kyautata yanayin aikin malamanmu. Allah yasa mudace
ReplyDelete