A yau ne committee na biyan gratuity wanda H.E Aminu Bello Masari ya kafa a karkashin jagorancin Alhaji Umaru Adamu, ya fara zama a Katsina state secretariat.
An dorawa
kwamitin alhakin tabbatar da biyan gratuity na ma'aikatan jaha da local
governments.
Indai ba'a manta ba a shekarar
bara anyi irin wannan biyan inda gwamnatin jahar katsina ta biya kudi naira
bilyan goma sha daya ga ma'aikata a matsayin kudin gratuity , cikin ikon allah
bana ma gashi za'a ci gaba daga inda aka tsaya.
Kwamitin dai zai duba da kuma tabbatar da cewa
ma'aikatan jaha, karamar hukuma da L.E.A da suka haura dubu hudu (4000) sun samu
kudinsu na ajiye aiki ba tare da wata tangarda ba.
Kwamitin wanda ya kunshi gogaggin ma'aikata kamar
su Alhaji Ibrahim Dabo Bujawa, SA Radio monitoring Mansir Ali Mashi, sai kuma
Auditor General na jaha dana local government ya fara aikinsa.
Kuma ana tunanin zai tantance
ma'aikatan domin biyan zunzurutun kudi naira bilyan bakwai da miliyan dari
hudu.
No comments:
Post a Comment