Gwamnatin Jihar Katsina, a karkashin jagorancin Gwamna Aminu Bello Masari, hadin guiwa da Babban Bankin Najeriya (CBN), ta kammala shirye shiryen habaka noman rani, musamman na Shinkafa a fadin Jihar nan.
Kan haka ne Gwamnati take gayyatar al'umma wajen taron kaddamar da
wannan shiri wanda idan Allah Ya yarda za ayi gobe Alhamis, 29/12/2015 a filin
Noman rani na Madatsar ruwa (Dam) dake garin Jibiya da karfe 11 na safe
Wannan shiri, da yardar Allah zai habaka tare da daga martabar harkar noman
rani da kuma tattalin arzikin manoma da kuma Jihar Katsina baki daya.
Muna rokon Allah (SWT) Yasa albarka a cikin wannan shiri,
Allahumma Amin.
Asali: SSA Social Media
No comments:
Post a Comment