Gwamnatin Jihar Katsina za ta mayar wa Ma'aikatan lafiya na Kananan Hukumomi da tsarin albashin CONHESS da aka dakatar a watannin baya.
Gwamna Aminu Bello Masari ya bayyana haka yau a Gidan Janar
Muhammadu Buhari, fadar Gwamnatin Jihar Katsina, bayan ya amshi rahoton Kwamin
da Gwamnati ta kafa domin tantance Ma'aikatan da suka cancanci amsar wannan
tsarin albashi. Ya kara da cewa wadanda aka tantance ne kadai za a mayar mawa
kuma biyan zai hada har da ariyas na watannin da su...ka gabata.
Tun farko a nashi jawabin, Shugaban Kwamitin Alhaji Salihu Maigari
Danjuma mni, ya bada rahoton cewa Kwamitin wanda ya kunshi har da Shuwagabannin
kungiyoyin kwadago, ya tantance Ma'aikata har 8,640 wanda kunshi;
1. 4,811 da suke aiki a asibitoci
2. 2,015 na bangaren samar da ruwa da tsabtar muhalli.
3. 1,038 na bangaren aikin gona
4. 776 na bangaren Ilimi da walwalar jama'a
2. 2,015 na bangaren samar da ruwa da tsabtar muhalli.
3. 1,038 na bangaren aikin gona
4. 776 na bangaren Ilimi da walwalar jama'a
Haka kuma sun sami Ma'aikata 1,056 wadanda suka rika amsar wannan
alawus ba bisa ka'ida ba, a saboda haka sun bada shawarar a mayar dasu kan
tsarin albashi irin na sauran ma'aikata.
Haka kuma sun bada shawarar da a inganta tsarin kula da duba
asibitocin tare da Ma'aikatan domin kauce ma fadawa cikin irin wannan matsalar
nan gaba.
Kwamitin kuma ya bada shawarar cewa duk wani mai dauke da takardar
kammala karatu (Statement of result) wadda ta kai tsawon shekara 10 to lallai
ne ya kawo Satifiket (Certificate) kafin a yarda da zaman shi Malamin lafiya.
Asali: AA Bawa
No comments:
Post a Comment