Wednesday, 27 July 2016

Karanta don Sanin Sabon Kwamishinan Kula Da Harkokin Addinini Na Katsina


Gwamna Aminu Bello Masari ya rantsar da Alhaji Tanimu Audi Bindawa a matsayin wakili a Majalisar zartaswa ta Jiha kuma Kwamishinan kula da harkokin Addini.

Bayan kammala rantsuwar, Gwamnan yayi kira gare shi da yasa tsoron Allah a duk abinda zai yi domin gobe kiyama Allah zai tambaye shi. Ya kuma hore shi da kada ya kawo ko saka banbancin akida a cikin aikin shi.


Gwamna Masari yayi mashi addu'ar Allah Yayi mashi jagoranci kuma Ya bashi ikon amsa duk tambayar da za ayi mashi gobe kiyama a kan wannan aiki da zai yi.

Source: SSA Social Media To Gov Masari

No comments:

Post a Comment