Wednesday, 27 July 2016

Gwamnatin Jihar Katsina Zata Fara Tantance Ma'aikatan Kwantaragi (Contract)

A taron ta na goma sha ukku (13) da ya gudana a dakin taro dake Gidan Janar Muhammadu Buhari, fadar Gwamnatin jihar Katsina, Majalisar zartaswa ta jiha a karkashin jagorancin Maigirma Gwamna Aminu Bello Masari, ta amince da bukatar da Hukumar Tsaron Kasa (Directorate of State Security Service) ta gabatar mata, ta bude Makarantar Sakandare a nan jihar.

Makarantar wadda za ta kasance makamanciyar irinta ta Hukumar 'Yan Sanda da take a garin Mani, an tanadar mata Matsugunni a Makarantar Sakandaren koyon kimiyya ta Gwamnati da ke a garin Musawa. Kuma da zarar an kammala shirye shiryen da suka kamata za a fitar da cikakken bayani musamman ta bangaren hanyar Shiga Makarantar da kuma inda daliban dake cikin Makarantar za su koma.

Haka nan kuma, Majalisar ta karbi rahotannin wucin gadi na tantance Ma'aikatan kananan hukumomi kashi na farko da na biyu, kuma da zarar an kammala hada rahoton za a kafa Kwamitocin sauraren koken wadanda abin ya shafa domin tabbatar da adalci.


Majalisar ta kuma amince da bukatar tantance Ma'aikatan da suke aiki a matsayin 'kwantaragi' (Contract), wannan zai sanya a tantance sahihancin yawansu, aikin da suke yi da kuma yanayin yarjejiniyar daukar su aikin da suke akai.

  Asali: SSA Social Media

No comments:

Post a Comment