Friday, 1 July 2016

Gov Masari Shin Biyan Haraji Ko Amsar Bashi? Katsina Mi nene Ma Fita

A kwana kin baya da su ka wuce, mai girma Gwamnan Katsina RT.Hon Aminu Bello Masari ya yi yaqinin cewa gwamnati za ta saka haraji ga masu yin sana’a da suka shafi ‘yan qurqura [Keke Napep/tricycle], Motocin haya [commercial vehicle] da kuma masu babura na haya [commercial motorcyclist].

Yin hakan ya faru ne don yadda gwamnati katsina ta shiga wani hali na rashin kudade dake shigowa asusun gwamnati. Wannan tsari a lokacin jama’ar jihar Katsina sun yaba mashi bisa  wannan tunani da kuma nufin za aiwatar da aikin. [decision].

To a lokacin kuma akwai wadansu  sace na jama’ar jihar Katsina wanda sun yi korafi a kan cewa, akwai banbanci tsakanin niyar aikatar [decision] da aiki da kuma fara aiwatar da wannan aikin,[implementation] ganin yadda kamun ludayin wannan gwamnati shine ta iya yin Magana mai zaqi, gwanin dade kamar duka kenan, amma aiwatar da aikin [full implementation] da abun da suka ce shine babban maqiyinsu a yanayi irin mulkinsu.


Yanzu haka an share watanni fiye da wata shadda [6] amma har yanzu gwamnatin bata dauki damarar fara aiwatar da wannan tsari [policy] na amsar haraji ga masu irin sanao’in da na zayyana a baya.

Wani abun al’ajabi shine irin yadda gwamnatin Masari ta duqufa wajen ranto kudin bashi da ruwa [interest] wanda yanzu haka majalisar dukoki ta jihar Katsina sun kara bashi dama don cin bashin Naira biliyan sha hudu [N14 Billion]. Jama’a ku sani fa, duk bashin da gwamnati ta ci to tana sadaukar da rayuwar mu ne da na ‘yayan mu wajen samun sakewa da walwala  a nan gaba, [Liquidating our future].

Domin idan ba a samu hanyoyi wanda za su kawu ma jihar Katsina kudi ba, to gwamnati dole ta shi gaba da cin bashi don tafiyar da aiyukan gwamnati, sannan duk wanda ya amshi mulki nan gaba, ba zai iya aiwatar da komai be sai dai biyan bashi ga jama’a na wahala matukar wahala.

Shi hangen nesa yana da kyau, idan baka da fasahar hangen nesa to za ka iya dauko kwararru wanda sun shahara wajen hangen nesa da tsare-tsare wanda zai taimaki jihar Katsina.

2 comments:

  1. Wannan yaskiya ne ya kamata gwamna ya duba Irin mutanen da ya ke ba mukamai.

    ReplyDelete
  2. Haka dai yakamata, domin za'a shiga wani hali idan ba'a gyara ba

    ReplyDelete