Allah
ya halicci dan adam yasa mashi tausayi da jinƙai, abinda akecema dan'adamtaka,
adabi'ar dan adam tunda can muna da tausai yajunanmu, hattana da kwarin dabbobi
dan adam na tausayinsu a dabi'ance da addinance.
Mu
musulmai tausayi da jin kai na daga cikin alamu da cikar imani na mutum,
amma fa a yanzu ta canja zani domin sammm bahaka bane musamman matasanmu da
manya masu budurwar zuciya babu sauran dan adamtaka atare dasu, kokari nasamar
ma da social media labari yasa sam bama tausayi ko jin kai ga yan'uwanmu ma
bare kuma dabbobin dake rayuwa atare damu.
Zakaga
mutane suna daukar hotonsu selfie da matattu na hadari ko wata mutuwa
wadda yakamata su tausaya amma sam tunanin neman like na friends yasa zukatansu
sun shagaltu da aikin duniya basa tuna inda wadannan dasuka mutu suka tafi
wanda ba makawa suma zasuje yanzu, yau, gobe ko jibi
, a'a wannan baya gabansu
ya salaaam Allah kashiryar damu.
Zakaga
mutane nadaukar hoto suna sallah tagaban liman mutane sun maida komai abin
talla hatta da addininmu da ibadarmu, gaskiyar magana munsaki layi muna kokarin
zama sokaye wawaye marasa tausai jin kai da duk wata alama dazata gwada mu
mutane ne masu sanin yakamata da tunanin gobe, munzama kauyawa gidadawa
dasunan wayewa .
Yakamata
mufarka mudawo cikin hayyacinmu dan wannan sam yasaba ma dabi'ar dan adam, raka
mamatanmu da wayoyi muna daukar hoto maimakon jimami dayimasu adduar dacewa da
masauki mekyau da nema masu gafara agurin Allah.
Da
haka nake kira ga al'umma dasuji tsoron Allah aduk kan al'amuranmu na yau da
kullum, Allah yasa mudace da rabo me amfani.
Allahu
aalam
Wabillahi taufeeq
Wabillahi taufeeq
26-07-2016
No comments:
Post a Comment