A daren jiya ne Litinin 6/6/2016 wadda tazo dai dai
da daya ga watan Ramadan hijra ta 1437 da misalin Karfe biyu na dare wani Yaro
mai suna Abdulaziz da ake ma lakani da Kunkuru ya dira gidan wani Yaro
makwabcinsa mai suna Yusha'u Aliyu dukkansu mazauna Unguwar Kofar bai dake
cikin garin Katsina da niyyar yi masa sata .
Lokacin da Shigar masa yayi ihu
barawo da niyyar neman dauki nan take ya daka masa wuka a qirji ya kashe shi ya
jefa shi a ramin masai ya kwashe wayoyinsa da kudi , Wanda a halin yanzu ana neman
yaron da yayi kisan.
Don haka Muna roqon jama'a Wanda ya ganshi ko yaji labarinsa da ya sanar da Hukuma mafi kusa . hoton yaron dake da dorowar rigar shine Wanda yayi kisan a gefe gudan gawar Wanda aka kashen ne.
Da fatan Allah ya gafarta masa ya
shirya mana zuriya ya bamu mafita ga wannan lamari.
No comments:
Post a Comment