Monday, 2 May 2016

Rahotun Tattaunawa Ta Tsakanin Leadership Newspaper Da Katsina Post Ta Buga Ba Gaskiya Bane.-Zango

Jaridar leadership tasa Kanun labarin hirar da su kayi da mai ba Gwamna Masari shawara akan harkokin siyasa kamar haka :"Jam'iyyar PDP bata da tacewa a shekara sha shidar da ta kwashe tana mulkin Jihar Katsina"
Kanun labarin da katsina post ta fitar dangane da wannan hira kamar yadda ta chanza kuma ta wallafa a bangon Jaridar ta da ta wallafa a 1:5:2016 tace " mai ba Gwamna Masari shawara ya hakikance akan cewa Marigayi Yar'adua da Shema basu tsinana komai ba a jihar katsina"

Labarai suna daga cikin manyan hajoji masu daraja a wannan duniya tamu. Yadda masu karatu suke sha'awar karanta labari da yadda zasu fahimci labari da kuma yadda sukanyi tsokaci dangane da labari mafi akasari ya danganta ga yadda mai bada labari ya tsara kanun labarinsa. Wannan yasa da yawa daga wasu masu karanta labari a wasu lokuttan sukan dogara kaco kam aKan kanun labari batare da karanta gangan jikin labari ba.

Tasirin samun labarai ta kafar yanar gizo musamman ta fejikan sada zumunta wato Facebook yana akan sahun gaba a wannan zamanin a wurin al'umma ganin yadda yake da saukin kawo labarai yadawa har ma da tofa albarkacin baki wannan ne ya haifar da matsalar yada jita jita idan har kafar yada labari ba sahihiya bace ko kuma yadda kafar data yada labarin batayi taka tsantsan ba wajen fadin sahihin zance dangane da labarin data bayar.


Cliqqmagazine.blogspot.com ta samu tattaunawa da Mai ba Gwamna Masari shawara akan harkokin siyasa kuma tsohon kakakin majalissar jihar Katsina Rt. Hon. Alhaji Usman Bala Zango ta wayar tarho dangane da hirar sa da yayi da wakilin Jaridar leadership sannan ta wallafa wacce itama katsina post ta dauka ta yada wanda hakan ya haddasa kace nace.

Jaridar leadership ta wallafa kanun labarin nata kamar haka "Jam'iyyar PDP bata da abinda zata nuna a shekara sha shidar da ta kwashe tana mulkin jihar Katsina"
A hirar da sukayi da Jaridar ba inda mai ba Gwamnan shawara kai tsaye ya kalubalanci Marigayi tsohon shugaban kasa Umaru Musa yar'adua ba kuma inda ya anbaci sunansa haka kuma ba inda ya anbaci sunan tsohon gwamnan Jihar Katsina Shehu Shema.

Da dan jarida ya tambayeshi "wani Lokaci a baya kai cikakken dan jam'iyyar PDP ne amma daga baya sai gashi kuma  kana Kan gaba wajen kalubalantar PDP to ko me ya kawo hakan?
Mai ba Gwamna Masari shawara sai yaci gaba da cewa kasan PDP tayi tabargaza da yawa. Wannan tasa basu iya sun tabuka abin azo a ganiba kowa yasan barnar da PDP ta aikata. Abinda ya tunzura ni nabar PDP kuwa shine almubazzaranci da kudin al'umma rashin tsaro  da kuma kasa cika alkawurran da suke daukar ma jama'a. Mutanen PDP ba da gaske suke ba.........

Wakilin na jaridar leadership ya kara tambayar sa shin baka ganin gwamnatin PDP data shude tayi kokari fiye da wannan gwamnatin taku?
Sai ya kada baki ya bashi ansa kamar haka anan ai masu zabe Sune alkalai kasan ai bazaka gina tituna ba kuma ga mutane na cikin yunwa da matsanancin talauci. Hakane gwamnatin PDP data shude ta giggina makarantu amma kuma zaka samu makarantun ba kujeru ba isassun malamai ba kayan da malaman da daliban zasu yi amfani dasu wajen koyo da koyarwa. Sai a yanzu ne wannan gwamnati mai ci yanzu ke kokarin shirye shiryen daukar kwararrun Malamai, tareda samar da isassun kujeru har ma da isassun kayan aikin koyo da koyarwa. Yanzu taya gwamnati zata gina kasuwa akan kudi N100 million ga Mutanen karkara a kowace karamar hukuma na kananan hukumomin 34 dake jihar nan bayan su Mutanen  nan suna cikin mawuyacin halin da ba gina kasuwa bane a gabansu?  PDP ba ruwanta da neman shawarar jama'a tanayin duk wani abu da take ganin shine dai dai awurinta batareda tuntubar jama'ar da take mulka ba.

Wannan wani bangare ne na yadda firar tasu ta kasance kuma idan akabi diddigin amsoshin sa za'a samu cewa suna Kan hanya don rashin kyautatawar jam'iyyar PDP ne yasa Mutanen jihar katsina sukayi mata mummunan kayi a zaben daya gabata

Dangane da kanun labarin da katsina post data wallafa game da wannan hirar wanda ya canza daukacin ma'anar hirar gaba daya kuma ya haddasa kace nace a cikin al'ummar jihar katsina mai ba Gwamna Masari shawara ya shaidama Cliqqmagazine.blogspot.com cewar sunyi mar kage saboda a firar da sukayi kaf ba inda ya anbaci abinda katsina post tace wai shi ya fada
Yayi kira da babbar murya ga masu wallafa labari ko kuma yan jarida da su guji yada labarin karya ko wanda basu da tabbas a kansa musamman ma labarin da basune ainahin wanda suka samo Shiba sannan ya kara da cewa lalle ne katsina post su rika tunrubar ita jaridar leadership kafin su chanza mata kanun labari




No comments:

Post a Comment