Bismillahi!
Salamu Alaikum., 'Danmajalissar jiha, (Katsina)
mai wakiltar karamar hukumar Funtua.
.
Tun da na ga fos din Malam Bashir Yahuza Malumfashi, wanda ya kattaba cewar an
kama Sani Funtua ta dalilin rubutun da yake yi a kan d'anmajalissar karamar
hukumarsu, musamman ma wata budaddiyar wasika da shi Hamzan ya rubutu zuwa ga
Abubakar Total din, nan take na kira zababben shugaban Kungiyar Marubuta jihar
Katsina (KMK) domin ganin abin ya shafi rubutu da marubuta ne, a nan yake
shaida mini ba shi gari. Jin haka ya sa na tuntubi Jami'in Hulda Da Jama'a,
wanda shi ma ba mazaunin cikin garin na Katsina ba ne, don haka sai na tafi ga
Sakataren na KMK, inda na yi sa'ar samunsa, na kuma shaida mishi halin da ake
ciki game da kes din na su Sani. Nan take ya fara bibiyar kadin lamarin cikin
zama da kazar-kazar. Bayan shi sai na sake tuntubar Ma'aji da kuma Mataimakiyar
Shugaba, su ma duk suka bazama don ganin lalubo bakin zaren. Kafin a jima dai
duk zababbun shugabannin KMK muka dukufa ta ko'ina wajen sasanta wannan rikici,
mun tuntubi abokan Sani don jin takamaiman abinda ke faruwa,
sun kuma ba mu
hadin kai wajen bayyana mana zahirin abinda ya wakana. Daga nan sai aka fara
motsi wajen ganin an saki shi Sanin da wani abokinsa da aka kama su tare.
Tashin farko Mataimakin Sakataren Tsare-tsare ya taso tun daga Matazu har
Katsina da safiyar yau juma'a, inda suka hadu da Sakatare domin ganawa da
d'anmajalissa, Abubakar Total. Sun samu ganawa da shi, kuma ya jaddada musu
cewar shi ba don wulakanci ko cin zarafi ya sa aka kama su ba, wai saboda a yi
musu tsakani ne kawai, kamar dai yadda ya kira abokin Sani, Janare Funtua ya
shaida mishi a shekaranjiya. Zaman nasu ya samu maslaha da haske kwarai da
gaske, tun da a nan take ya kira ofishin yan sandan da su Sani suke, ya shaida
musu kawai a sake su, komai ya wuce, amma fa a ja musu kunne don kar su sake
shiga duk wata sabga tashi (Kasancewar ba jam'iyyarsu daya ba), har ma ya nuna
cewar akwai wanda yake zargin shi ke tura Sani don yi mishi ''Fitsara!''
.
Daga karshe dai, kuma a takaice an saki Sani Hamza Funtua da kuma yin sasanci
tsakaninsu da d'anmajalissa Abubukar Total a dazu da ranar nan.
.
Hakika Kungiyar Marubuta jihar Katsina ta taka muhimmiyar rawa a wannan kes
din, duk da cewar Sani Funtua ba mambanta ba ne, sai dai da yake an ce ruwan da
ya ci Doma, ba shi barin Awai, shi ya sa ba mu yi kasa a gwiwa ba wajen ganin
komai ya sanyaya, sai fatar Allah kara sanyaya shi.
.
... A madadin d'aukacin shugabanni da mambobin kungiya muna mika godiyarmu ga
Danmajalissa, Abubakar Total da jami'an yan sandan da suka ba mu hadin kai
wajen ganin komai ya daidaita, muna godiya da wannan karamci.
.
Muna fatar Allah kiyaye gaba.
.
Mataimakin Sakatare;
Hafiz Adamu Koza, a madadin daukacin shugabannin Kungiyar Marubuta jihar
Katsina (KMK).
No comments:
Post a Comment