
Wani Dan Majalissar dokoki na jahar Katsina mai
wakiltar Funtua yasa yan sanda sunyi awon gaba da wani marubuci a farfajiyar
Facebook mai suna Sani Hamza Funtuwa saboda wata budaddiyar wasika daya
rubutama dan Majalissar.
Dan haka muna kira ga hukumar yan sanda datasan
cewa ba an kirkireta bane danta kare muradun masu madafun iko. Ba zaluntar
mutane akace tayi ba, a'a, kare hakkinsu akace
tayi, irin hakkin Sani Hamza Funtua da aka shiga.
Muna kira ga shuwagabannin Majalissar Dokoki na
jaha dasu kira abokin aikinsu da yashiga hankalinshi! Yaza'ayi an zabeshi
yakare hakkin mutane kuma yazama yana samasu takunkumi? Idan wanda aka zaba
yayi dokoki dan Jin dadin al'umma, kuma yazama shine kan gaba akan karya doka?
Muna kira da aja mashi hankali kuma yasa asaki Sani Hamza Funtua.
Harwayau munakira ga gwamnatin jaha data shiga
wannan magana saboda anshiga hakkin danta bakan ka'ida ba.
Munada shedu inda Dan Majalissar yake barazana ga
Sani Hamza akan rubutun dayayi.
Muna kira ga duk wani Dan Katsina dakuma abokanmu
na sauran Jahohi dasu taimaka wurin wannan yakin kwato yancin dan'uwan mu danya
zama darasi akan masu tinanin aikata haka.
No comments:
Post a Comment