A lokacin da 'Yan Naijeriya ke fama da zingar ciwon
tabarbarewar tattalin arziki da kuma karancin man-fetur da kasar ke fuskanta,
tabarbarewar tattalin arzikin wanda daya biyo baya sakamakon faduwar farashin
man-fetur warwas a kasuwar duniya da kuma faduwar darajar naira wacce ta
durkusawa dalar Amirka da darajarta ke hauhawa , wasu 'yan kasuwa a kasar sun
zabi su gina shekarsu ta jin dadi da tara dukiya ta hanyar kumbura farashin
kayan abinci dana wasu amfanin gida fiye da gona da iri, koda kau yanayin ta
ake ciki na tsadar kayan bai shafi wasu kayan ba. Wasu kuma daga cikin 'yan
kasuwan da tsadar kayan ta shafi kasuwancinsu, sunyi kama da masu maraba da
yanayin marar dadi , domin kuwa kakarsu ta yanke saka, a inda suke fakewa da
labaran-dola-tayi-sama su ci karensu ba babbaka, wato su hauda farashin kaya ko
aiki sama, linki-ba-linki ta yanda zasu sami riba mai tsoka, samun kudi cikin
sauki ba tare da wata zufa ba. Wato wata sabuwar hanya ce ta tara
dumbin dukiya da ta bullo musu - tsuntsu daga sama gassashe. Zaka ji wani
lokacin suna korafi a baki cewa aikinsu ko kasuwancinsu zai durkushe idan har
wannan yanayi na narkewar tattalin arziki ya cigaba a kasar to amma a zukatansu
sun san ba haka bane. Basa fatan wannan yanayi na wahala ya kare don gudun
romon ribar da suke kwasa ya kare.
A wannan yanayi mai wahalar gaske ga 'yan Naigeriya wanda
ya kamata ace suna nuna tausayi, ragi, hakuri da soyayya ga juna, abin
takaicine ganin irin yanda wasu 'yan kasuwa suka maida talaka saniyar tatsa.
Kadan ne daga cikin 'yan kasuwar ke nuna tausayi da ragi. Ko shakka babu
gaskiya ne cewa farashin kayan masurufi dana wasu abubuwa ya karu a Naigeriya ,
kuma wasu yan kasuwan na bakin kokarinsu da nuna tausayi wajen taimakawa jama'a
domin samun sauki kuma gaskiya ne cewa wasu daga cikin 'yan kasuwan,
kasuwancinsu bazai iya jure wuyar da ake ciki ba idan har wannan hali da ake
ciki ya cigaba tsawon lokaci, to amma kuma ba karya bane cewa da yawa daga
cikin 'yan kasuwan zasu iya taimakawa wajen rage wahalhalun da talakawa suke
ciki idan suna nuna kishin kasa da tausayin talaka. Kwanaki mun samu rahoton
cewa wani dan kasuwa dake a jihar Kano yayi kira ga 'yan kasuwa 'yan uwansa da
suji tsoron Allah su tausayawa jama'a inda ya bayyana cewa ba kowani kayan
amfani bane tsadar kayayyakin ta shafa ba, to amma wasu daga cikin 'yan kasuwa
nayin amfani da damar cewa dola tayi tsada su kuntatama jama'a. Zan bada misali
da farashin ruwan leda, hakika farashin kudin leda ya karu sosai kusan linki
biyu.
A kwanakin baya ne bada dadewa ba, wata kungiyar 'yan
kasuwa masu siyar da ruwan-sha na leda da akafi sani da 'fiyo wota' suka hadu
kuma suka yanke shawarar kara farashin kudin ruwa daga N50 zuwa N70 ko N80 duk
jaka daya. Wani rahoto daya biyo bayan kammala tattamnawarsu akan karin
farashin shine, wani daga cikin 'yan kasuwan a kungiyar bai lamince da karin
farashin ba, inda ya bayyana cewa zai cigaba da siyar da ruwan shan akan tsohon
farashi. Shin tambaya anan itace, shin kyauta yake samar da ruwan kuma bai cin
riba ko kadan? Koko hakuri yake da ribar da yake samu marar yawa wacce a da mai
dumbin yawa ce kafin hauhawar farashin leda wacce ake siyowa daga kasashen waje
domin sarrafa ruwan cikin leda? Ni a iyakar sani na da tunani na hakurine yake
da riba marar yawa ba don wai baya samun riba ba ko kadan. A ra'ayina da tunani
yana da tausayi da kishin kasa.
A takaice, abinda ke faruwa a halin yanzu shine , jakar
ledar fiyo wota daya ana siyar da ita ne akan N100 yanzu a jihar Katsina abinda
bai taba faruwa ba abaya. Abin takaici shine 'Yan Naijeriya sun kasance suna
labartawa juna da korafi akan yanda cin hanci da rashawa ke so ya latata kasar
da juyayi akan yanda wasu manyan jami'an gwamnati na kasar ke cika aljihunsu da
dukiyar al'umma su bar talakawa cikin wahala da talauci to amma abin mamaki
shine , wasu 'Yan Naigeriya sunyi kama da wa'anda suka manta da halin da irin
wadannan 'yan kasuwa masu zuciyar dutse suke kokarin jefa su. Ya kamata
shuwagabannin addinai, hukumomin gwamnati da masu zaman kansu su dage da maida
hankali wajen fadakar da mutane akan tausayi, soyayya da kishin kasa . Ya
kamata ace 'yan Naijeriya su rungumi juna da tausayi a irin wannan yanayi na
wahala. Haka kuma ya kamata gwamnatin kasar ta sake kara linka kokarinta da
zage damtse wajen ganin wannan yanayi na wahala da ake ciki an wayi gari ya
gushe kuma talakawa na murmushi kamar yanda tayi alkawari.
No comments:
Post a Comment