Sunday, 24 April 2016

Shin Ko Gov. Masari Na Tattauna Batutuwan Da Suka Kamata Wajen Taron Al'ummumi


A ranar Asabar 23-04-2016, mai girma Gwamna RT. Hon Aminu Bello Masari yayi tattaunawa daya saba yi duk bayan lokaci kadan, A taron wanda ya kunshi manufar wanda yake kunshe da bayanai da bayyana ma al’umar yadda gwamnati ke sarrafa kudin d ake shigowa da kuma kuma yadda ake kashe wadannan kudade.

Haka zalika, ya bayyana ma al’umah irin ayyuka na Alheri daya ke yi, sannan kuma bayyana irin tsare tsare na ayyuka da gwmantin shi ta tanada za tayi ma al’umma.

To amma wani hanzari ba gudu ba, shin ko mai girma Gwamna Masari yana yi ma al’umma a wajen yin taron bayanin dalillai da yasa ya bada da umurni ga masu aikata gyran makarantu na gwamnati a kana nan hukumomi da ke Batagarwa da Ajiwa da a fadada  ajin karatu wanda zai dauki dalibai dari da hamsin (150).


Abun tambaya a nan shine, shin wannan tsari yayi dai dai ga tsarin da ya da ce da zuba dalibai a aji? Koko tayaya Malami zai koyar da dalibai guda 150 kuma su fahimta, su gane cikin natsuwa abun da malami yake koyawa? Shin ko su wa ke  ba mai girma Gwamna shawara akan wannan fanni?

Abu na biyu shine, shin ko mai girma Gwamna Masari yakan yi bayyana gamsas she ga al’ummah wajen hanyoyi daya tsara domin kawo ma jihar Katsina kudade ta hanyoyi daban daban. Domin jama’a sun ciga damuwa akan irin halin da matsala da za’a fuskanta  idan ba an samu wata hanya mafi a’ala kuma mai yuwowa da za a bijiru domin samun kudade.

 Allah ya taimaki gwamnatin jihar Katsina. 

No comments:

Post a Comment