Monday, 25 April 2016

Ko Kaji Abdulhadi Bawa Yayi Shar Hi A Kan Nasarorin Gwamnatin Masari

A duk lokacin da aka sami canjin Gwamnati to tabbas sabuwar Gwamnati za ta gaji dumbin abubuwa daga tsohuwar Gwamnati, kama tun daga hakkokin ma'aikata (albashi, fansho, garatuti, karin girma da sauran su), ayyukan da aka kammala, wadanda aka fara amma ba a kammala ba sai kuma wadanda aka ce za ayi amma ba a fara ba.
A nan Jihar mu ta Katsina ma haka abin ya wakana.
Da yardar Allah, za mu bi wadannan abubuwa sannu kan hankali, daya bayan daya, domin sanin halin da wannan Gwamnati a karkashin jagorancin Dallatun Katsina, Alhaji Aminu Bello Masari ta taras da wadannan abubuwa sannan kuma muyi bayanin irin kokarin da tayi wajen ta kai dauki yadda kamata, duk kuwa da matsi na na karancin kudin shiga da ake fuskanta.
BANGAREN SAMAR DA RUWAN SHA (Kashi na Daya)
A bisa ga halin da matatun ruwa na Jihar suke ciki a daidai lokacin da wannan Gwamnati ta kama aiki, a iya cewa ba su taba shiga cikin mummunan yanayi irin haka ba, domin kuwa rahoton da Ma'aikatar ruwa ta Jiha ta bayar ya nuna cewa babu wata matatar ruwa da take samar da abinda ya kai rabin abin da ya kamata ta samar.
Duk kuwa da cewa ko da suna aiki yadda ya kamata ba za su iya cimma bukatun al'umma ba wanda a yanzu ya kai kimanin lita 120 a kan kowane mutum. Dududu abinda suke samarwa a manyan garuruwan jihar bai kai kashi goma cikin dari (10%) ba.

Daga cikin matsakaitun ma'aikatun ruwa guda arba'in da daya (41) da ke a fadin Jihar, wadanda aka taras suna aiki basu kai kashi Ashirin cikin Dari (20%) ba.
Sannan kuma rashin tsayayyenamfani da kishi ya sa mafi yawancin ma'aikatun ruwa na karkara sun zama basu da wani amfani.
Tsarin samar da ruwa na birane ya kumshi garuruwan Katsina, Daura, Funtua, Dutsinma, Malumfashi da Jibia. Dukkan wadannan garuruwa, ban da Daura, suna samun ruwa ne daga madatsun ruwa (Dams) da ke a wannan Jiha, ita kuwa Daura an yi mata tsarin amfani da rijiyoyi ne (borehole).
Ma'aikatar ruwa ta garin Daura ta share sama da shekaru Hudu (4) ba ta aiki, ita kuwa ta Malumfashi ta yi sama da shekaru Bakwai (7) bata motsa ba.
Saboda tsufa da lalacewar kayan aiki, ma'aikatar ruwa ta Ajiwa wadda kuma ita ce take birnin Katsina da kewaye ruwa tana samar da kasa da kashi Sittin (60%) na abinda ya kamata ta samar.
Saboda karancin wutar lantarki da kuma man Disel da kananan hukumomin su ke bayarwa, Ma'aikatar ruwa ta Jibia tana aikin awa Shidda (6) a rana ita kuma Dutsinma tana awa (8). Ita kuma Funtua tana yin aiki na awa Goma sha Biyar (15) a rana idan akwai wutar lantarki daga kamfanin Wuyar.
A karshen tattaunawar da Gwamna Masari yayi da jami'an Ma'aikatar ruwa ta Jihar, ya bada umurnin a kawo mashi lissafin adadin kudin da ake bukata domin gyaran ma'aikatun ruwa na Daura da Malumfashi, domin wadannan garuruwa su ci gaba da samun ruwa ba tare da bata lokaci ba.
A cikin watan sha daya na shekarar da ta gabata (November 2015) aka kammala aikin gyaran ruwa na garin Daura wanda yaci kimanin Naira Miliyan Talatin Talatin da Hudu, kuma Alhamdu lillah, yanzu a duk rana garin Daura yana samun a kalla Lita miliyan biyu da rabi na ruwa a duk rana ta Allah.
A halin da ake ciki kuma yanzu, aikin da aka bada na ma'aikatan ruwa na garin Malumfashi da aka bada kan kudi Naira Miliyan Dari da Arba'in da Daya shi ma ya kammala, domin tuni ruwa ya samu a garin Malumfashi.
A cikin kwana Dari da hawan Gwamna Masari aka gyara matsakaitan ma'aikatun samar da ruwa na Rahamawa Abattoir, Dutsin Safe da kuma Sabuwar Unguwa duka a nan cikin garin Katsina.
Zancen kuma da ake yanzu, Gwamnati ta bada aikin gyaran Ma'aikatar ruwa ta Ajiwa wanda ya hada harda matatar ruwan, wannan zai sanya ta rika samar da ruwa kamar asalin yadda aka tsara ta tun farkon kafa ta. Wannan aiki za a yi shi a kan kudi Naira Bilyan Daya da Miliyan Dari Tara (N1.9b).
Famfunan samar da ruwa masu amfani da hasken rana guda Sittin da Hudu (64) da kuma na tukajihaa-tuka guda Dari da Biyu (102) aka gyara a yankuna daban daban na wannan jiha.
Mu hadu a kashi na Biyu in shaa Allah


No comments:

Post a Comment