Sunday, 2 September 2018

Gaskiya ne Adam.A Zango yasaki matarsa yan kamarun?



Da Dumi-duminsa Fitaccen Jarumin Hausa Film Adam A Zango ya zama gwauro ya saka matar yar asalin kasar kamaroon wacce ya aura shekarun baya.

Mujallah Hausa Film ta ruwaito cewa jarumin ya saki matartasa yanzu yana zaman gwauranta.


Idan bamu manta ba jarumin sai da saki matarsa Maryam AB Yola wacce ta haska a film din NAS wanda jarumin shiya bada umarnin a Film din sannan ya auro wannan matar daya saki yanzu.
Idan bamu manta ba cewa kwanakin bayayana mutane sukaita cece-kuce akan cewa jarumin yana auri saki, ya fito ya kare kansa yake fadi mai daki shiyasan inda ruwa yake masa zuwa harma abokinsa Nura M Inuwa yake ganin ya wayar da kan jama,a cewa Adam A Zango baya auri saki wannan sharri ne kawai na makiya.

Yanzu haka dai an fara hasashen cewa da wacce jarumin zai maye gurbin matar tasa Fati Washa ko Zainab Indomie domin kuwa hasashe ya nuna cewa kamar jarumin yana soyayya da wayan nan jarumawa.

Idan mai karatu na biye damu jiya mun kawo muku cewa shima sallau ya saki matar Furera bisa wani binciki nasa da yayi kuma ya gano wasu boyayyayun abubuwa marasakyau a tattare da jarumar wanda hakan ne yasa ya saketa.

Mujallah Film ta wannan satin dai tana dauke da zafafan labarai


No comments:

Post a Comment