Babbar
Jam'iyyar adawa ta PDP a Jihar Katsina ta Sha alwashi Kayar da shugaban kasa
Muhammadu Buhari da kuma Gwamna Aminu Bello Masari a kakar zabe mai zuwa ta
2019.
Shugaban
jam'iyyar PDP na Jihar katsina, Alhaji Salisu Yusuf Majigiri ya bayyana haka a
lokacin da yake tattaunawa da manema labarai, jim kadan bayan kammala taron da
jam'iyyar ta gudanar da masu son tsayawa takara 'yan majalisun jiha da kuma
shugabanni jam'iyyar na kowane mataki, wanda ya gudana a helkwatar jam'iyyar da
ke Katsina.
Majigiri ya
kara da cewa "Ina da yakinin jam'iyyar mu ta PDP za ta samu nasarar lashe
zabe mai zuwa a kowacce kujera har da ta shugaban Kasa duk da dan asalin jihar
Katsina ne. Dalili kuwa shi ne babu wani abun azo a gani ko kuma wani aiki da
jam'iyyar APC ta yi wa al'ummar jihar Katsina da za su fito su yi yakin neman
zabe da shi, sai dai sun jefa al'ummar cikin halin fatara da talauci da kuma
rashin aikin Yi ga matasa.
Alhaji
Salisu Yusuf Majigiri ya cigaba da cewa duk mutumin da ke jihar katsina ya
shaidi irin ayyukan alheri da jam'iyyar PDP ta shimfida a cikin shekarun goma
Sha shidda da muka kwashe muna mulki da kuma gagarumin cigaba da jihar Katsina
ta samu da kuma ayyukan da Gwamnatin tarayya ta yi a Jihar. Shi yasa al'ummar
jihar suke da tabbacin idan ta dawo a 2019 za ta cigaba da ba yayansu ilmi
kyauta da kuma gudanar da ayyukan da zai inganta rayuwar su.
Daga karshe
ya yi ga yan takarkaru na jam'iyyar PDP da suke sayen form na kowacce kujera su
zamanto ayi siyasa ta fahimta, babu batanci ga juna. A tafi a nemi jamaa duk
Wanda Allah ya ba nasarar lashe zabe, wanda bai samu ba ya ba shi goyan baya
domin ganin mun amshi kafatanin kujerun mu wato tun daga sama har kasa da yardar
Allah a 2019.
No comments:
Post a Comment