Friday, 20 October 2017

SANARWA | Jami'ar Al-Qalam Ta Fara Tantance Takardun Dalibai Na Zangon 2017/2018


Jami’ar  Al-Qalam da ke Katsina na sanar da wadanda suka nemi shiga Jami’ar, cewa anfara tantance takardun su na Zangon karatun shekarar  Alif Dubu Biyu da Goma Sha Bakwai zuwa Goma Sha Takwas (2017/2018).

Saboda haka ana shawartarsu da su gaggauta shiga adereshin yanar gizon jami’ar watau a www.auk.edu.ng domin samun Karin bayanin ranar da zasu zo da takardunsu.

Har ilayau, Makarantar Gaba da Digri na Farko da ke Jami’ar watau (School of Postgraduate Studies) na sanar da jama’a cewa ta fara saida Form na daukan dalibai na Zangon karatun shekara Alif Dubu Biyu da Goma Sha Bakwai zuwa Goma Sha Takwas (2017/2018).

Ana iya samun Karin bayani a cikin shafin yanar gizo na Jami’ar a forms.auk.edu.ng

Duk biyan kudaden za ayisune ta yanar gizo da taimakon katin banki na ATM watau MasterCard, Visa ko kuma Valve Card.

 
SANARWA

Hukumar Jami’ar Al-Qalam, Katsina

(Jami’ar  Musulunci ta farko a Nigeria)   

No comments:

Post a Comment