Da farko dai banso ace abin yakai haka ba, domin nasan irin halin mutanenmu basa daukar komai da wasa, dagaske suke yinkomai ko na kirki ko na banza.
Tun farkon
bullar wannan kanu, tunbayan cin zaben shugaban kasa muhammadu buhari,
nayi tunanin masu ruwa da tsakin yakin dayake babatun karewa zasu fito su
nisanta kansu dashi, suja mashi kunne, su gayamashi cewa wannan tsari
daya biyo ba me bullewa bane yama kiyayeshi tun da wuri, amma a rashin
dacewa da samun mutane masu irin tunanina awancan yanki yasa sammm suka nuna
halin ko in kula suka barshi yaci gaba da cin karensa babu babbaka.
Wannan sakaci ne ya haifar da halin da muke ciki yanzu tundaga bude gidan radiyon biyafura har yazuwa kamashi, da sakoshi da zanga-zanga matasa mara ma'ana, masu cutar da mutane.
Wannan sakaci ne ya haifar da halin da muke ciki yanzu tundaga bude gidan radiyon biyafura har yazuwa kamashi, da sakoshi da zanga-zanga matasa mara ma'ana, masu cutar da mutane.
Abinda yaja
hankalina yanzu dayasa dole ince wani shine abinda ya faru kwanannan na kaima
hausawa mazauna yankin dasuke cewar nan ne kasarsu ta biyafura hari suna
kashesu suna kona masu dukiyoyi.
Nayi
tunanin igbo sunyi karatun ta nutsu su kula cewa idan wannan abun na kaima
yan'uwanmu hari shine suke ganin hanyar da zata sa abasu kasar biyafura, to
lallai basu ba kasar biyafura har abada kuwa, domin idan anci gaba da
kone-konen nan har takai mutanen arewa suka tashi dan maida martani to inyamurai
sune zasuyi asarar dukiya fiye da kashi 80% cikin 100 na dukiyar da za'a asara
yayin wannan arangama, inya murannan dukiyoyin su ne cike da kasuwannin
mu, da lungu da sako na kauyukanmu, amma kash saboda daqiqanci da jahilci
irin nasu sun kasa fahimtar haka, su fito su nisanta kansu da wannan kanun nan,
gomnoninsu su hanashi shiga jahohinsu domin kare dukiyoyin yan'uwansu
dake kasuwanci dukkan lungu da saqo na arewacin nigeria.
Idan dai
har saboda hadin kai da tunanin bazasu kwarema dan'uwansu baya ba ya sa sun
kyaleshi yana iskanci to, mu yan arewa ba cima zaune bane, muna da abincin da
zamuci har nan da shekara biyar, dan haka mu ba tsoran araba kasar nan muke, ko
yau akace za'a jefa kuri'ar raba gardama to ni zanzabi a rabata kowa ya kama gabansa
susha mansu, muci doyarmu, masararmu, dawarmu, wakenmu, shanunmu da dukkan
abinda muke nomawa, har ake tunkaho da najeriya na ciyar da afrika, mainakon
ace arewa na ciyar da afrika.
Dan haka
lokaci yayi dazamu bude idonmu, duk shegen dayace mana kule muce ma shege
cassss,
Amiru
Danamarya
14-09-2017
No comments:
Post a Comment