Friday, 4 November 2016

Katsina | Kwamitin Kula Da Ruwan Sha Yakai Ziyara A Gidan Ruwa Na Dutsin-ma Mai Shekaru 42 Da Ginawa


Kwamitin kula da ruwan sha na jihar Katsina ya kai ziyarar gane ma ido a garin Dutsinma.

Makasudin ziyarar shine don ganewa matsalolin da irin hanyoyi da za a bi don magancewa da farfado da Gidan ruwan dake Dutsinma.  Kwamitin ya samu shugabancin Abubakar Matazu wanda a inda yayi alkawarin mika sakamakon bincikin su zuwa ga mai girma Gwamna Aminu Bello Masari.

Gidan ruwa na Dutsinma ya shekara 42 da budewa, kuma yanzu haka dakunan magani, da enginan genareta duka basayi.

Ana shi jawabin, shugaban Gidan ruwa na Dutsinma Alh Yahaya ya mika godiya ga gwamnati Katsina ganin yadda take ta kokari don raya wannan Gidan ruwa.
A satin da ya gabana, Mai girma gwamna Masari ya fuskanci barazana a yayin daya kai wata ziyara na rufe gasar wasan kwallo da akayi a garin Dutsinma. A inda mutanen garin Dutsinma manya da yara suka fara mashi aho da jifa da duwatsu suna furta cewa “bamayi bama su” ganin yadda gwamnatin tashi tayi watsi da matsalolin jama’ar Dutsinma.

Cin ko wannan turniki ne ya jaza wannan ziyara na kwamitin ruwa ta kai ziyara zuwa Gidan ruwa na Dutsinma?

No comments:

Post a Comment