Taron zanga-zangan ya hada da tsofaffin mata da
matasa daban daban daga kowane sashe a cikin jihar Katsina wanda su na ta
korafi akan irin yadda Dr Mustapha Inuwa yayi baba-kere da handama da kuma
butulce ma irin alkawarin tallafa masu da gwamnatin RT. Hon Aminu Bello Masari
ta dauki alkawarin niyar taimaka masu.
Wakilin Cliqqmagazinehausa.blogspot.com
ya fahimci cewa matasan da taron jama’a da suka hallarci wannan zanga-zanga sun
bauta ma wannan gwamnati wajen yakin ta na ne man cin zabe da ya gudana na
shekarar 2015, Wanda suka yi yar jejeniya ta cewa gwamnati zata tallafa masu da
hanyoyi da za su fara sana’oi iri daban daban.
To amma yanzu shekara daya kenan babu alamar cika
masu wannan alkawari da gwamnati tayi. Wasu kuma daga cikin su sun ce Sakataren
gwamnati Dr Mustapha Inuwa ya shigo yayi baba-kere a maganar wanda har ma yana
yin korafi da cewa “su mutanen banza ne, Yan iska marasa abun yi, kai ma har
Gidan yari [prison] zai sa a kai su idan basu maida hankali ba ga cewar su amma
a wani video da ke yawo a yanar gizo-gizo na sadawar Facebook”.
Da yawansu sun dan gana halaiyar Mustapha Inuwa da
abun kyama da zalunci wanda yasa ma irin hakan tasa marigayi shugaban kasa
Umaru Musa Yar’adua ya kure
shi daga Sakataren gwamnati a lokacin ya na gwamnan jihar Katsina.
Daga bisani ma wasu sun yi aman na da cewa ishara
ce Allah ya ke nuna ma mutanen Katsina akan irin butulci da suka yi ma Gwamna
Shema wanda gashi tun ba aje ko ina ba gwamnatin APC da irin su Dr Mustapha
Inuwa Sun Fara butulce wa jama’ar da su ka sha wahala wajen zaben su.
To, Ko ya zata kaya? Gwamna Masari ne kawai zai iya
bada tabba tattaciyar amsa akan ko…. gwamnatin shi zata cigaba da Mustapha
Inuwa koko zai yi bincike iya binciki akan yadda mutanen katsina ke kalubalantar
halaiyar Mustapha Inuwa wajen kamanta adalci da gaskiya.
No comments:
Post a Comment