Kungiyar marubuta ta kasa reshen jihar Kano (ANA) ta karrama wasu shaihunnan malaman Jami'a da suka yiwa harkar rubuce-rubuce hidima tsawon shekaru.
Taron karramawar na cikin taron da kungiyar ta saba yi
duk shekara mai sunan satin marubuta,
wanda akan dauki sati guda cur ana gudanar da jawabai da mukaloli akan yadda za
a bunkasa harkar rubutu a kasar nan.
Taron na bana mai martaba sarkin Kano Muhammadu
Sanusi II ya bude taro da kansa a Ranar 6/12/2018.
A Ranar lahadi 9/12/2018 aka rufe taron da bada
kyaututtuka daga cikin wadanda aka baiwa kyauta akwai wasu makarantun boko da
su ka yi nasara ga wata gasa da kungiyar ta marubuta tayi a tsakanin makarantun
jiha akan adabi.
Sai kuma wasu fitattun mutane da kungiyar tace suna
yiwa harkar rubutu, hidima a kasar na tace mutanen tsaye suka wajen ganin adabi
ya bunkasa, suma wadanda aka baiwa
adabin an kasa su kashi biyu.
kashin farko su ne Farfesa Abdallah Uba Adamu da
Farfesa Mustafa Ahmad Isa da Farfesa Adamu Idris Tanko da Farfesa Aliyu Kamal
da Dakta Bukar Usman da Dakta Bala Muhammad da Dakta Ismaila Bala da Injiya Y.Z
Ya'u da Zaharadeen Ibrahim Kalla da Alhaji
Badamasi Burki sai Muhammadu Danjuma Katsina.
Danjuma Katsina shi ne mawallafin jaridar Taskar
Labarai dake bisa yanar gizo, wadda kan kawo rahotannin musamman, akan
Al'amurran yau da Kullum.
Daga cikin
marubutan da ka karrama akwai wadanda Allah yayi masu rasuwa, amma sun
yi ma adabi hidima kafin rasuwarsu.
Su ne marigayi
Hadi Alkalanci da malam Balarabe Sango da malam Balarabe Sari da Rukayya
Maikafi da Abdullahi Mukhtar Yaron Malam.
Akwai Kashi na biyu da aka karrama sun hada da:
Malama Maryam Ali Ali da Aminu Ladan Alan waka da Maimuna
Beli (wadda taci Gasar adabi na BBC a Bara) da Danladi Haruna.
An yi taron a dakin taro na babban dakin karatu na
jihar Kano Mai suna Murtala Muhammed kuma ya samu halartar baki daga ciki da
wajen Kano.
Daga Katsina akwai Alhaji Dikko Bala Kofar Sauri da
Lawal Danja da Alhaji Sallau Arawa Co-ordinator na Hajiya Mariya Bala Usman da
DG NPA sun yi wa Danjuma Kara sun hallarta.
Hon Mansur Ali
Mashi (Dan majalisar Mashi/Dutsi) ya dau nauyin 'Yan kungiyar Writer's Bureu,
Katsina chapter wadanda suma sun halarta don yiwa Danjuma Kara.
No comments:
Post a Comment