Mafi akasarin alumma sukan yi mafarkin abinda ke ran
su, Maana suna fadin abinda suka fi tsana a rayuwar su fiye da komai.
A shekara 2015 Hon.Umar Tata ya fito neman kujerar
gwamnan jahar katsina a PDP daga Nan ya koma APGA Mai alamar Zakara, Umar Tata
yayi iyakar kokarin shi ya kuma bi dukkan hanyoyi domin ganin ya samu nasarar
wannan Zabe, Amma sai gashi yazo na karshe ,Maana shine mafi karancin kuru'un.
engr. musa tashuni da sen.yakubu Garba Lado danmarke suna gaban shi a Kuri'u.
Uncle Umar Tata idan mukai kididdiga zamu ga cewa
yawan Kuri'un da ya samu a jahar katsina baya wuce ace kowa ne akwatin zabe ya
samu kuri'uTara (9)
Idan muka dauki kaf Kuri'un da uncle Umar Tata Ya Samu
kaf jahar katsina sune 42,302 Wanda muna da Rumfunan zabe guda 4,902. Mu
kaddara cewa kaf akwatinan zaben dake gare mu na jahar katsina guda 4,902 kowa
ya zabi Tata To Kuri'un basu wuce ya
samu Kuri'u Tara Tara (9)(9) kowane akwati.
Masu iya magana cewa "mi jiya Tayi bare yau"
a baya Hon. Umar Tata da kanshi yake nema mawa Kudi, A Wancen lokacin da kudin
shi jibge a Jika baya jiran wani attajiri ya bashi.
2015 Yana sabon fuska ga alumma ,baa San halin shi ba,
baa San waye shi ba, alumma na ganin shi matsayin uba, suna hangen cewa yazo ya
taimake su, Kuma ba kudi ko mulki yake nema ba. Alumma na ganin cewa da kanshi
yazo ba aiko shi akayi ba, Kuma ba yaron wani bane, shine Mai gidan kan shi da
kan shi yazo.
A Wancen lokacin Alummar jahar katsina basu da
tabbacin cewa gwamnati ko wani attajiri ya bashi kudin yazo neman kuri'a.
Lokacin bai yi fada da wasu yaran shi ba, bai fada da
wasu Jama'ar gari ba, bai je yayi magana ya chanza ba,(A Kori yunwa).
A 2015 kaf kowa na ganin shi a matsayin wani tauraro
Yana tare da dukkan abinda za yayi amfani dashi wajan kawo Kuri'u Amma ya kasa
samun kuri'a AKALLA 12 kowa ce rumfa .sai yanzu??
Gare ku APC nasan kunsan dukkan abinda yake ciki da
Kallon kallon da kuke mashi na biri da ayaba, Amma Yana da kyau mu karu da
shawarar juna ta hanyar yin amfani da kalaman Malam bahaushe na cewa
"dukkan Wanda yace zan baka RIGA to dubi ta wuyan shi" Hon. Tata ko
Rumfar da yake zabe bai taba ci ba
balantana yaci rumfar waje.
Gare ku yayan PDP nasan wannan maganar da Uncle Tata
yayi magana ce Mai ban dariya magana ce da kuka dade Kuna Jin irin ta tun daga
zaben mashi/dutsi na cewa zaya bada naira milyan goma goma ga dukkan inda suka
kawo ward din su da Kuma ya ga lokaci ya kure sai yaje ya jawo Mana fada.
Kada in jaku da nisa yau Umar tata tsauri ba shike ne
mama kanshi kuri'a ba gov.aminu Bello masari Yake nema mawa idan har a chan
baya ya kasa samun kuri'a AKALLA sama da guda goma (10) kowace rumfa, yau Ina
bukatar ganin yadda zayace kada takai dozin har masu biye da Dan Tata suji
dadin maganar suna rantsuwar cewa tata na iya haka.
To nidai nace duk tatsuniya ce......
Comr.Nura Adam Kankara Tina
DG campaign buhari/masari MOST GO organization
No comments:
Post a Comment