Wednesday, 5 September 2018

Yadda aka tsinci wani yaro a Makabartar sabuwar Danmarna da za ayi tsafi da shi a Katsina


A safiyar Talata hudu ga watan Satumba a Inwala dake cikin garin Katsina iyalen Alh Kabir Yau Al-Baba wanda ke aiki a gidan Radiyon Vision fm suka tsinci kansu a wani irin halin mai tashin hankali da saka damuwa akan satar yaron su Aliyu mai shekara goma sha ukku da barayi masu satar yara suka sace shi.
Wakilin Cliqq Magazine Hausa ya tattaunawa da mahaifin Aliyu a inda ya baiyana wa wakilmu duk yadda abun ya faru.

Shi dai Kabir Al-baba yace “a ranar Talata misalin karfe bakwai (7am) na safe, ina zaune a kofar gida, sai ga yaro na Aliyu ya fito, na tambaye shi ina zai je, yace mani sai sawo kalaci ne a nan makwabta. Bayan ya dawo sai ya kara fitowa har ma nake ce masa kada yayi nisa domin lokacin zuwa makaranta ya kusa”.
Daganan sai wakilin mu ya tambaye shi a dai dai wani lokaci ne ya farga da cewa yaron shi Aliyu baidawuba.
“Kamar Yadda na ga yama, tun fita ta biyu da yayi ban sake jin motsin shi balle na saka shi a cikin ido har wajen karfe tara na safe, wanda yakamata a ce ya dawo ya tafi makaranta, amma kasan abun ka da yara, sai nake tunanin ko ya bi abokanan sa sun tafi wasa ko kuma sun tafi makaranta tare. Da naga misalin karfe sha biyu na rana yayi, sai na tambayi abonkansa ko sun ganshi a makaranta, wanda suka ce mani gaskiya basu ga Aliyu ba, tofa daga nan sai ni da iyali na muka fantsama nemanshi tare da bada sanarwa a wajen ‘yan sanda, gidanjen yata labaru na radiyo da talabijin tare da kuma gayama ‘yan uwa da abokan arziki”.
”Amma Allah cikin na shi ikon sa, wurin lokacin sallar Magariba sai wani yaro ya tsunto Aliyu a wajen sabuwar makabartar Dan Marna wadda ke goron gida yana tafiya amma ba baki, ganin hakan sai ya rike mashi hannu ya na ta binshi kamar akuya har sai da ya maido shi gida”.
Abun da wakilinmu ya gano shine, bayan Bakin shi bude, ya baiyana ma iyayen shi cewa a lokacin da ya fito daga gida, sai ya ji an kwala masa kira, sai wani mutum ya kira shi ya bashi Naira Ashirin yace masa ya biyo shi, suna tsakar tafiya sai ya rataya masa wata sarka a wuyanshi, har sai da suka yi nisa sannan mutumin ya samar masu abun hawa.

Yaron da aka sace ya shaida ma wakilinmu cewa, shi dai wajen hanyar Batsari cikin wani daji aka kaishi, kuma a gidan akwai yara kanana da manyan duk an masu askin kwalkwali, suna sanye da tufafi farare da kuma wani shaida da aka yi masu a kawunan su.
Wakilin mu ya ga kwalkwalin da aka yi ma Aliyu da kwalba wanda ya nuna cewa saura kiris ya rasa rayuwar shi ga masu satan yara don asiri ko neman duniya.
A karshe mahaifin Aliyu yayi kira ga iyaye da su kula da yaransu sosai musamman ma wajen hana su karbar kudi ko alawa daga wajen mutanen da basu sansu ba.

No comments:

Post a Comment