Ranar 24 ga
Satumba, 2005 ne, Allah S.W.T.) ya dauki ran daya daga cikin fitattun 'yan
gwagwarmaya a Najeriya dama Afirika wato Dokta, Yusufu Bala Usman. Marigayi
Dokta Yusufu Bala Usman ya yi shura ne wajen caccakar akidar jari-hujja, ya
kuma yi wallafa-wallafe da dama akan matsalolin Najeriya dama Afirika.
Kadan daga cikin littatafan da ya wallafa sun hada da:
Transformation of
Katsina,For the Liberation of Nigeria, Religious Manipulation in Nigeria, misrepresentation
of Nigeria da sauran su.
Sabboda
irin gudunmuwar da wannan bawan Allah ya bada a lokacin rayuwarsa, inda ya
sadaukar da rayuwasa wajen ganin talaka ya samu 'yanci, kungiyar Muryar Talaka
Reshen jihar Katsina za ta gudanar da babban taron tunawa da shi.
Taron da aka
tsara za a yi ranar Litinin, 24 ga Satumba,2018 a Makera Motel, Katsina
wanda ya zo daidai da cikar marigayin shekara 13 da rasuwa.
Zai kunshi gabatar
da mukalu daga fitattun masana kamar Farfesa Aliyu A. Jibia na Jami'ar tarayya
dake, Gusau, da Dokta Aliyu Muhammad Muri na Jami'ar Alqalam dake Katsina da
Dokta Musa Ahmed JIbril dake sashen nazarin tarihi da tsaro dake Jami'ar Umaru
Musa Yar'adua, Katsina.
A lokacin
da yake zantawa da wannan kafa, babban sakataren kungiyar Muryar Talaka na
kasa, Comrade Bishir Dauda Sabuwar Unguwa Katsina, ya ce tuni suka kammala
dukkan shirye-shirye dangane da wannan taro,kuma ya ce kishin Najeriya ne yasa
kungiyar ta ga ya dace ta shirya wannan taro.Sannan ya kara da cewa, dama ba
yau kungiyar Muryar Talaka ta saba shirya taruka masu ma'ana irin wadannan ba,
abin da ya ce na taimakawa sosai wajen samun shugabanci nagari a Najeriya.
No comments:
Post a Comment