Thursday, 12 May 2016

JANYE TALLAFIN MAN FETUR- Malam Mansur

Abin Da Mutane Suka Kasa Fahimta Kamar yadda gwamnatin Tarayya ta bada Sanarwar cire tallafin Man Fetur a wannan rana ta Laraba 11-may-2016 kamar yadda Minista a ma'aikatar Man-Fetur din Mr. Ibe Kacikwu ya sanar. Abinda wasu mutane basu fahimta game da wannan al'amari ba shine. Shi Man bawai ana nufin farashinsa zai kama daga Naira 145 kwatsam a ko ina bane.

A'a Abinda ake nufi anan shine Masu Gidajen man 'yan kasuwa an lamince musu su shigo da man daga duk inda suke so. Amma dukkan Man 'yan kasuwa zasuna sayar dashi akan Farashin da bazai taba haura Naira 145 ba.

Amma kuma gidajen Man mallakin gwamnati irinsu: NNPC, TOTAL da sauransu, zasuna sayarwa alumma akan farashi Mai rahusa. Idan har gwamnati ta sakarwa 'yan kasuwar Mara suka shigo da Man Barkatai kuma ta sanya ido sosai akan 'yan kasuwar akan yadda suke gudanar da hada-hadarsu. To Insha Allahu Man zai zama tamkar "Ledar Pure Water akan titunan mu". Kaga kenan 'yan kasuwar Mai zasu karu, kuma duk abinda yayi yawa to karshensa zai fadi ne warwas .

Misalin abinda yake faru yanzu a kasuwannin Man Fetur din ta duniya. . Hasalima Idan mukayi La'akari da Abinda ya faru ga Kamfanonin wayar Salula a Nigeria. A baya Layin wayar Salula guda daya taka wato "MTEL". wadda mallakin gwamnati ne.
Amma tun daga Lokacin da gwamnati ta sakarwa kamfanonin Layukan wayar Salula mara su zo su kafa a Nigeria irinsu MTN, V-MOBILE, GLO da sauransu. Da farkon farawa sai da ake sayar da Layin waya Kusan Naira 13,000.  Amma yanzu da abubuwan suka yawaita gashi Layin waya Harda akwai na N50 ma. wani Lokacin ma Layin wayar kyauta za'a baka. Kaga kenan Idan Allah ya yarda Shima wannan Bangare na Man-Fetur din yan kasuwa zasu shiga zasu shiga gasar shigo dashi ta ko ina, babu kama hannu yaro. Wadda daga karshe Farashin Man zai dinga rikirkitowa a kowanne Lokaci da ikon Allah. ~ Muna da tabbacin Buhari bazaiyi abinda zai cutar da alummar wannan kasa ba.

Ya Allah muna rokonka ka sa wannan mataki da gwamnatin Nigeria ta dauka akan Man fetur yazama shine silar kawo karshen wahalhalun da alummar kasa kan Sha wajen samun man. Allah ka sanya wannan itace hanyar da zata sanya man ya zama ana sayarshi har N50.

Allah ya kara kawo mana yalwatuwar Arziki amen

No comments:

Post a Comment