Monday, 24 September 2018

An daga ranar dawowar majalisar dokoki ta kasa daga hutu


Akawun majalisar dokoki ta Tarayya Sani Omonori ya sanar da daga ranar dawowar majalisar dokoki ta tarayya da ya hada da majalisar dattawa da na wakilai.

A wata takarda da ya fitar ranar Lahadi Omonori ya ce an yi haka ne saboda zabukan fidda ‘yan takara da jam’iyyun kasar nan za suyi a wadannan kwanaki.

Idan ba a manta ba majalisar kasa za ta dawo hutu ne ranar 25 ga watan Satumba.

Yanzu an daga dawowar zuwa 9 ga watan Oktoba kamar yadda sanarwan ya fadi.
Premiumtimeshausa.

No comments:

Post a Comment