Mutane biyar ne suka rasa rayukan su wajen amsar Zakah a Gidan Ma’a Gafai da ke Rafindadi a cikin garin Katsina.
Wakilin Cliqq Magazine Hausa ya ziyar ci
Unguwar Rafindadi a inda ya sa mu ganawa da wadansu bayin Allah da kan idanun su
abun ya faru.Sun shai dawa wakilin mu cewa abun ya
faru da safe ne a yayin da aka fara rabon Zakka wanda dumbin jama’a suka zo don
su alfana da wannan zakka.
Hakan ya jawo matsatsi wanda mutum biyar
daga cikin masu amsar Zakkar suka rasa rayukan su wadan su da dama kuma suka ji rauni.
Daga cikin mamatan guda biyar din yara ‘yanmata
ne.
Wakilin mu ya shaida mana cewa ita
wannan Zakka kudin Naira 500 ne kachal ake badawa.
Cliqq Magazine Hausa ta samu labarin
cewa mai girma Gwamna Aminu Masari ya ziyar ci wadan da suka ji raunuka a Gidan
asibiti.

No comments:
Post a Comment